Connect with us

Labarai

Za A Samarda Tsaro Lokacin Bukin Sallah A Nasarawa – Kwamishina

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce an samar da isassun matakan tsaro domin tabbatar da gudanar da bukukuwan Sallah ba tare da tangarda ba a jihar.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Umar Shehu Nadada ya bayyana haka a wata sanarwa da ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai a garin Lafia babban birnin jihar.

 

Sanarwar ta bayyana cewa Kwamishinan ‘yan sandan a lokacin da yake taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan na bana tare da yi wa dukkan musulmi fatan bukukuwan Sallah lafiya. Ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da su yi amfani da lokacin bukukuwan domin yin addu’o’in zaman lafiya da ci gaban jihar da kasa baki daya.

 

Kwamishinan ‘yan sandan ya yi kira ga malaman addini, masallata da mazauna jihar da su ba ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro hadin kai, domin ya tabbatar da cewa an yi kokarin inganta tsaro a lokacin bikin sallah karama.

 

Sanarwar ta kuma umurci dukkan kwamandojin ‘yansanda na yankin da shugabannin sassan da kuma jami’an ‘yan sanda na sassan jihar da su rika sanya ido domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a, da samar da tsaro a duk wuraren ibada da na shakatawa da kuma kai samame a wuraren da aka gano akwai matsala.

 

Don haka kwamishinan ‘yan sandan ya umarci al’ummar jihar da su kasance masu zaman lafiya da gudanar da bukukuwa cikin kwanciyar hankali.

 

Idan kuma wata matsala ta taso, ana kira ga jama’a kada suyi kasa a gwiwa wajen kiran wadannan lambobin waya kamar haka: 08036157659, 08032564469, 08112692680 da 08104441179.

Rel/Aliyu Muraki/Lafia/Wababe

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara