Connect with us

Labarai

‘Yan Sanda Sun Ceto Dan Kasar Sin Da Aka yi Garkuwa Da Shi A Kwara

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta ceto wani dan kasar Sin wato China ami suna  PengChao Zhang da wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da shi a Eiyenkorin da ke karamar hukumar Asa ta jihar.

 

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan DSP Ejire-Adeyemi Toun ya fitar, ya ce wasu ‘yan bindiga shidda  sun yi garkuwa da Mista PengChao Zhang, wanda aka fi sani da Williams Kaka a lokacin da yake  da abokan  kasuwancinsa da a wani massukin  baki a ranar 10 ga Maris, 2024.

 

Sanarwar ta ce, rundunar da ‘yan tare da hadin gwiwar jami’an sa kai sun aiwatar da jerin bincike  da suka kai ga ceto dan kasarSin din.

 

Sanarwar ta bayyana cewa, tuni aka sada shi  da iyalansa ba tare da wani rauni ba.

 

Ta kara da cewa, wannan nasara da aka samu na nuna jajircewar rundunar ‘yan sandan jihar wajen tabbatar da tsaro  ga dukkan mazauna jihar da maziyartan jihar.

 

Rundunar ‘yan sandan ta kum bukaci jama’a da su sanya ido tare da kai rahoton duk wani abu da ba su yarda da shi ba  ga jami’an tsaro domin daukar matakin gaggawa.

 

Ali Muhammad Rabi’u

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara