Labarai
‘Yan Sanda Sun Ceto Dan Kasar Sin Da Aka yi Garkuwa Da Shi A Kwara
Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta ceto wani dan kasar Sin wato China ami suna PengChao Zhang da wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da shi a Eiyenkorin da ke karamar hukumar Asa ta jihar.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan DSP Ejire-Adeyemi Toun ya fitar, ya ce wasu ‘yan bindiga shidda sun yi garkuwa da Mista PengChao Zhang, wanda aka fi sani da Williams Kaka a lokacin da yake da abokan kasuwancinsa da a wani massukin baki a ranar 10 ga Maris, 2024.
Sanarwar ta ce, rundunar da ‘yan tare da hadin gwiwar jami’an sa kai sun aiwatar da jerin bincike da suka kai ga ceto dan kasarSin din.
Sanarwar ta bayyana cewa, tuni aka sada shi da iyalansa ba tare da wani rauni ba.
Ta kara da cewa, wannan nasara da aka samu na nuna jajircewar rundunar ‘yan sandan jihar wajen tabbatar da tsaro ga dukkan mazauna jihar da maziyartan jihar.
Rundunar ‘yan sandan ta kum bukaci jama’a da su sanya ido tare da kai rahoton duk wani abu da ba su yarda da shi ba ga jami’an tsaro domin daukar matakin gaggawa.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
