Connect with us

Kasuwanci

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 15 Sun Raunata 3 A Jihar Kebbi

Published

on

Gwamnatin jihar Kebbi ta jajanta wa al’ummar Waje da ke karamar hukumar Danko Wasagu sakamakon harin ‘yan bindiga da ya yi sanadin mutuwar manoma 15 tare da jikkata wasu 3.

 

Mataimakin gwamnan jihar, Sanata Umar Abubakar Tafida, ya mika sakon ta’aziyyar gwamnati tare da bayar da tallafin Naira miliyan 24 ga iyalan wadanda suka mutu da wadanda suka jikkata.

 

Ya bayyana hakan a matsayin kokarin da gwamnatin jihar ke yi na tallafawa iyalan wadanda suka mutu da wadanda suka jikkata a wannan lokaci mai cike da kalubale.

 

Sanata Abubakar, ya bayar da tabbacin cewa gwamnatin jihar za ta dauki matakan da suka dace don magance matsalar rashin tsaro, tare da baiwa manoma damar gudanar da ayyukansu cikin aminci.

 

Shugaban karamar hukumar Danko Wasagu, Alhaji Hussaini Aliyu Bena, ya tabbatar da cewa an kashe manoma 15 tare da jikkata wasu 3 a harin da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai.

 

Hakimin Waje, Alhaji Bala Danbaba, a lokacin da ya yaba wa gwamnatin jihar bisa wannan ziyarar da kuma tallafin kudi, ya bayyana cewa, iyakar Danko Wasagu da jihohin Neja, Zamfara da kuma Sokoto na haifar da matsala, inda ya yi kira da a kara inganta tsaro domin toshe wadannan hanyoyin shiga.

 

Abdullahi Tukur

Labarai

Labarai5 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara