Labarai
Yadda Aka Kashe Jagoran ’Yan Ta’addan Katsina Da Yaransa

Sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe Maikusa, wani kasurgumin dan ta’adda da ke jagorantar hare-hare a Jihar Katsina.
Maikusa ne mataimakin wani fitaccen dan ta’addan da ya addabi jama’ar Jihar Katsina Modi Modi, wanda ake nema ruwa a jallo.
Daraktan hulda da jama’a na rundunar sojin Najeriya, Manjo-Janar, Onyema Nwachukwu ne ya sanar cewa sojojin sun hallaka Maikusa da wasu ’yan ta’adda uku ne a ranar Litinin, a tsakanin kananan hukumomin Kurfi da Safana da ke jihar bayan bata kashin da sojin suka yi da ’yan ta’addan.
Ya ce, wannan gagarumin aiki ya yi nasarar kawar da ’yan ta’addar da suka jima suna addabar al’ummar yankunan.
Ministan Tsaron Najeriya, Muhammad Badaru Abubakar, ya ce sojoji a cikin ’yan watannin da suka gabata sun kashe akalla manyan jagororin ’yan tada kayar baya bakwai a kasar.
Ministan ya bayyana haka ne a wata hira da manema labarai a Jaji ranar Talata.
Ministan wanda ya kai ziyarar aiki, ya gabatar da jawabi ga sojojin da ke halartar wani taron kara wa juna sani da kwalejin yaki da ta’addanci da ’yan ta’adda.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
