Connect with us

Labarai

Ramadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsoro Tare da Tallafawa Marasa Galihu

Published

on

Daga Yusuf Zubairu Kauru

Sarkin Kauru da ke Jihar Kaduna, Alhaji Zakari Ya’u Shehu Usman, ya yi kira da a kara inganta tsaro a yankin, inda ya bukaci hukumomi su rika sa ido sosai kan masu ba da bayanan sirri, tare da samar wa jami’an tsaro isasshen tallafi domin su gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

Mai Martaba Sarkin ya bayyana hakan ne a yayin taron bude baki na watan Ramadan na shekara-shekara da ake gudanarwa a ranar 15 ga watan Ramadan a fadarsa da ke Kauru.

Sarkin ya kuma bukaci al’umma su kara dagewa da yin addu’o’i domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar nan, yana mai cewa manoma na fuskantar kalubale masu yawa sakamakon tashin farashin kayayyakin abinci, lamarin da ke shafar rayuwarsu da harkokin noma.

Ya kuma jaddada muhimmancin karfafa dankon zumunci musamman a wannan wata mai alfarma na Ramadan, tare da karfafa gwiwar jama’a da kungiyoyi su rika taimakawa marasa galihu ta hanyar bayar da abinci da sauran tallafi.

Hakazalika, Sarkin ya yabawa Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, kan ayyukan ci gaba da gwamnatinsa ke aiwatarwa wadanda ke kawo sauyi mai ma’ana ga al’ummomin Karamar Hukumar Kauru.

Daga karshe, ya bukaci mazauna yankin su ci gaba da bai wa jami’an tsaro hadin kai, tare da dagewa da yin addu’o’i domin samun dawwamammen zaman lafiya a fadin kasar nan.

Rediyon Najeriya  Kaduna ta rawaito cewa Sarkin ya rufe taron da addu’o’in samun zaman lafiya da cigaba, tare da rokon Allah ya kara wa masarautar  daukaka.

Labarai

Labarai2 hours ago

Ramadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsoro Tare da Tallafawa Marasa Galihu

Daga Yusuf Zubairu Kauru Sarkin Kauru da ke Jihar Kaduna, Alhaji Zakari Ya’u Shehu Usman, ya yi kira da a...

Labarai2 hours ago

Gwamnatin Jigawa Ta Sha Alwashin Bin Kadin Shari’ar Walida Abdulhadi

Daga Usman Muhammad Zaria  Gwamna Umar Namadi ya tabbatar da cewa Gwamnatin  Jigawa za ta bi sawun shari’ar sace ‘yar...

Labarai1 day ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi1 day ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai1 day ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Mafi Shahara