Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa ta Amince da Shirin Ciyarwar Watan Ramadan na Bana

Published

on

Daga Usman Muhammad Zari

Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da gudanar da shirin ciyar da jama’a na buda-baki (Iftar) na shekarar 2026, da nufin tallafa wa marasa galihu, tare da tabbatar da cewa al’ummar jihar sun samu abinci mai gina jiki a lokacin watan Ramadan mai alfarma.

Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi, Dr Nura Ibrahim Kazaure, ne ya bayyana hakan jim kaɗan bayan taron majalisar zartarwa ta jihar da aka gudanar a Government House Dutse.

A cewarsa, shirin da aka amince da shi ya tanadi kafa cibiyoyin ciyarwa guda 640 a faɗin jihar.

Ya ce hakan ya haɗa da kafa cibiyoyi biyu a kowace daga cikin mazabun siyasa 287 da ke cikin ƙananan hukumomi 27 na jihar, da kuma cibiyoyi na musamman a manyan makarantu, gidajen gyaran hali, da cibiyoyin jin ƙai domin tabbatar da cewa kowa ya amfana da shirin.

Dr Kazaure ya nuna cewa ana sa ran shirin zai rika samar da abinci ga mutane sama da  264,600 a kowace rana,

A tsawon watan Ramadan, ana sa ran shirin zai samar da abinci sama da miliyan 23 da dubu 800 wanda za mutane sama da miliyan 7 da dubu 900 za su amfana.

Kazaure ya ce an tsara shirin ne domin samar da abinci mai gina jiki da inganci ga Musulmai masu azumi da sauran marasa galihu, tare da tallafa wa gidaje masu ƙaramin ƙarfi da kuma mutanen da ke fuskantar matsin tattalin arziki.

Ya ƙara da cewa shirin zai ƙarfafa zumunci a tsakanin al’umma, tausayi, da ɗaukar nauyin juna, tare da ƙara tallafa wa shirye-shiryen  zamantakewa da rage talauci da gwamnatin jihar ke aiwatarwa.

Sai dai Dr Kazaure ya bayyana cewa majalisar ta umarci a bi ƙa’idojin inganci sosai wajen sayo kayan abinci, girkawa da kuma rabawa.

Kwamishinan ya ƙara da cewa za a kafa kwamitocin sa ido a matakin jiha, ƙananan hukumomi da kuma unguwanni domin tabbatar da an aiwatar da shirin yadda ya kamata tare da rabon adalci.

Ya buƙaci shugabannin al’umma, cibiyoyin addini, ƙungiyoyin matasa da ƙungiyoyin fararen hula su bayar da cikakken haɗin kai domin tabbatar da nasarar shirin tare da kiyaye tsari a duk cibiyoyin ciyarwar.

Ya ƙara da cewa wannan shirin na jin ƙai da haɗa kan jama’a ya kuma shafi ma’aikatan gwamnati na jihar, waɗanda su ne ginshiƙin aiwatar da manufofin gwamnati a fannoni daban-daban.

 

 

Labarai

Labarai17 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara