Labarai
Gwamnatin Jigawa ta Amince da Shirin Ciyarwar Watan Ramadan na Bana
Daga Usman Muhammad Zari
Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da gudanar da shirin ciyar da jama’a na buda-baki (Iftar) na shekarar 2026, da nufin tallafa wa marasa galihu, tare da tabbatar da cewa al’ummar jihar sun samu abinci mai gina jiki a lokacin watan Ramadan mai alfarma.
Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi, Dr Nura Ibrahim Kazaure, ne ya bayyana hakan jim kaɗan bayan taron majalisar zartarwa ta jihar da aka gudanar a Government House Dutse.
A cewarsa, shirin da aka amince da shi ya tanadi kafa cibiyoyin ciyarwa guda 640 a faɗin jihar.
Ya ce hakan ya haɗa da kafa cibiyoyi biyu a kowace daga cikin mazabun siyasa 287 da ke cikin ƙananan hukumomi 27 na jihar, da kuma cibiyoyi na musamman a manyan makarantu, gidajen gyaran hali, da cibiyoyin jin ƙai domin tabbatar da cewa kowa ya amfana da shirin.
Dr Kazaure ya nuna cewa ana sa ran shirin zai rika samar da abinci ga mutane sama da 264,600 a kowace rana,
A tsawon watan Ramadan, ana sa ran shirin zai samar da abinci sama da miliyan 23 da dubu 800 wanda za mutane sama da miliyan 7 da dubu 900 za su amfana.

Kazaure ya ce an tsara shirin ne domin samar da abinci mai gina jiki da inganci ga Musulmai masu azumi da sauran marasa galihu, tare da tallafa wa gidaje masu ƙaramin ƙarfi da kuma mutanen da ke fuskantar matsin tattalin arziki.
Ya ƙara da cewa shirin zai ƙarfafa zumunci a tsakanin al’umma, tausayi, da ɗaukar nauyin juna, tare da ƙara tallafa wa shirye-shiryen zamantakewa da rage talauci da gwamnatin jihar ke aiwatarwa.
Sai dai Dr Kazaure ya bayyana cewa majalisar ta umarci a bi ƙa’idojin inganci sosai wajen sayo kayan abinci, girkawa da kuma rabawa.
Kwamishinan ya ƙara da cewa za a kafa kwamitocin sa ido a matakin jiha, ƙananan hukumomi da kuma unguwanni domin tabbatar da an aiwatar da shirin yadda ya kamata tare da rabon adalci.
Ya buƙaci shugabannin al’umma, cibiyoyin addini, ƙungiyoyin matasa da ƙungiyoyin fararen hula su bayar da cikakken haɗin kai domin tabbatar da nasarar shirin tare da kiyaye tsari a duk cibiyoyin ciyarwar.
Ya ƙara da cewa wannan shirin na jin ƙai da haɗa kan jama’a ya kuma shafi ma’aikatan gwamnati na jihar, waɗanda su ne ginshiƙin aiwatar da manufofin gwamnati a fannoni daban-daban.
-
Labarai6 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai5 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai2 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai5 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai6 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai4 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
