Labarai
Kungiyar Marayu Ta Yi Kira Ga Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gina Wa Mata Cibiyar Koyan Sana’o’i.
Kungiyar Marayu ta Jam’iyyatu Tukaful Aytam ta yi kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna ta taimaka mata wajen gina cibiyar koyarda sana’o’i.
Shugabar kungiyar, Malama Rabi’atu Adam Isma’il ta yi wannan kiran a wurin taron rabawa Marayu Kayayyaki da ya gudana a harabar ofishin kungiyar dake Barnawa Kaduna

Ta ce samarda cibiyar zai taimaka wajen samarwa mata da matasa hanyar sana’o’i domin su dogara da kansu.
Har ila yau, ta ce samarda cibiyar zai taimaka wajen kawarda ayyukan shaye-shaye a tsakanin matasa da kuma rage radadin talauci a tsakanin al’umar yankin.
Da take tsokaci a wurin taron, shugabar kungiyar Nisa’us Sunnah dake Barnawa Kaduna, Malama Amina Namadi tace Kungiyar Jam’iyyatu Tukaful Aytam ta kwashe shekaru 14 wajen ayyukan kulada marayu ta hanyar tara taro-sisi a tsakanin mambobinta.
Ta kara da cewa, a haka kungiyar ta dauki alhakin kulada marayu 10 tun suna kanana har suka kai wani mataki ta hanyar sanyasu a makaranta da ciyarda su da tufatarda su tareda koya musu sana’o’in hannu.
Wasu daga cikin waɗanda suka amfana da tallafin Hauwa Usman da Usman Bala, sun godewa Kungiyar bisa wannan yunkuri, tareda addu’ar samun daukaka don kaiwa ga babban matsayi.

Kayayyakin da kungiyar ta raba su ne, kayan abinci da masarufi ga marayunta 12, sai kuma kayan Sallah ga sauran marayu maza da mata 60.
Khadija Kubau
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
