Connect with us

Ilimi

Jihar Bauchi Za Ta Yi Aiki Da Hukumar Kula Da Almajirai Ta Kasa

Published

on

Gwamnatin jihar Bauchi za ta hada gwiwa da Hukumar Almajiri da Yara da basa zuwa Makaranta don daukar nauyin karatun yara marasa galihu.

 

Gwamna Bala Muhammad na jihar Bauchi ya bayyana kwarin gwiwar sabbin shugabannin Hukumar Almajirai da Ilimin Yara da ba su zuwa Makarantu na kasa wajen biyan bukatun yaran da abin ya shafa a kasar nan.

 

Ya bayyana hakan ne a lokacin da ya gana da Babban Sakataren Hukumar Dokta Muhammad Sani Idris wanda ya ziyarce shi a gidan gwamnati da ke Bauchi.

 

Gwamna Muhammad ya ce idan aka yi la’akari da tarihi da dimbin gogewar Sakataren Zartaswa, za a tunkari kalubalen Almajiri da yaran da ba sa zuwa makaranta.

 

A baya dai Sakataren zartaswar ya ziyarci Uwargidan Gwamnan Jihar Bauchi, Dakta Aisha Bala Muhammad wadda ta nemi goyon bayan hukumar wajen shigar da ilimin boko a cikin manhajar karatun almajirai karkashin aikinta na Pet project na gidauniyar AlMuhibba da kuma gidauniyar Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

 

Dokta Aisha Muhammad ta ce da irin dimbin gogewar da shugaban Hukumar Almajiri da Ilimin Yara da ba su zuwa Makarantu ke da ita, ta yi fatan hadin gwiwar da ake so da za ta tsara makomar miliyoyin yara masu rauni a kasar nan.

 

Sakataren zartarwa ya bayyana jin dadinsa da tarbar da aka yi masa a yayin ziyarar tare da bayar da tabbacin bada hadin kai don cimma manufofin.

 

Alhassan Usman/Wababe

Labarai

Labarai1 day ago

Ziyarar Shugaba Tinubu Zuwa China Ta Yi Nasara

  Ziyarar Shugaba Tinubu zuwa China Ta Yi Nasara, da kuma Shaida Wa ‘Yan Najeriya Mazauna China, Yi Alkawarin don...

Labarai2 days ago

Sabon Tsarin Albashi: Majalisar Kano Ta Amince da Karin Kasafin Naira Biliyan 99

Majalisar Dokokin Kano ta amince da ƙarin kasafin kudi na N99bn da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya aike mata domin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Zamfara Ta Musanta Jita-Jitar Bayar Da Kudi Ga ‘Yan Ta’adda

  Gwamnatin Jihar Zamfara tayi watsi da jita-jitar da ke yawo cewar tana shirin bayar da kudi ga wasu sanannun...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Dauki Matakan Gaggawa Don Wadata Man Fetur da Farashinsa

  Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Ɗauki Matakai Masu Ƙarfi don Magance Samuwar Man Fetur da Farashi a Faɗin Najeriya A...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nemi Hadin Gwiwar Afirka da China Don Bunkasa Tattalin Arziki

  Shugaba Bola Tinubu ya yi kira da a ci gaba da hadin kai tsakanin Afrika da Sin, yana mai...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya ta Amince da Tsare-tsare Don Yakar Rashin Abinci Mai Gina Jiki

  Daga: Bello Wakili Ministan Tsare-tsare na Lafiya da Walwala ta Jama’a na kasa, Muhammad Ali Pate, ya jaddada muhimmancin...

Labarai3 days ago

ACF Ta Ce Babban Kalubalen Arewa Yanzu Shi Ne Rashin Tsaro

Kungiyar Tuntubar Arewa, wato Arewa Consultative Forum (ACF) ta ce a halin yanzu, batun da ya fi damun al’ummar arewacin...

Labarai3 days ago

Hukumar NOA Ta Yabawa Majalisar Jihar Nasarawa Wajen Samarda Dokoki Masu Amfani ga Jama’a

Hukumar Wayar da Kan Jama’a da Fadakarwa ta Kasa (NOA) ta yaba wa Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa bisa ga kafa...

Kasuwanci4 days ago

Shugaba Tinubu Ya Gana da Firayim Ministan Sin, Ya Ce Afirka Na Da Damar Zuba Jari da Haɓaka

  Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya ce Afrika na da manyan damammaki wajen zuba jari, ci gaba, da haɓaka tare...

Labarai4 days ago

Tinubu Ya Jajantawa Jihar Yobe Kan Rashe-Rashen Rayukan da Aka Yi a Tarmuwa

  Shugaba Bola Tinubu ya jajantawa gwamnati da al’ummar jihar Yobe kan rashin rayukan da aka yi a Mafa a...

Mafi Shahara