Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Kayan Abinci Ga Dubban Iyalai A Jihar Kebbi

Published

on

Gwamnatin Tarayya ta fara rabon kayan abinci da na gina jiki ga dubban marasa galihu da kuma masu larurar nakasa a Jihar Kebbi.

Ministan Kasa a Ma’aikatar Harkokin Jin-ƙai da Rage Talauci, Alhaji Yusuf Tanko Sununu, wanda ya kaddamar da rabon a Birnin Kebbi, ya ce shirin ya nufin tallafa wa al’ummomin da suka fi rauni waɗanda bala’o’in jin-ƙai suka shafa a jihar.

Yusuf Sununu ya bayyana cewa shirin ya haɗa da rabon kayan gina jiki da magunguna ga asibitoci, cibiyoyin kula da yara, da sauran rukunonin da ke bukata. Ya ƙara da cewa za a kai irin wannan tallafi zuwa sauran mazabun sanatoci na jihar.

Ya ce shirin ya yi daidai da ajandar  sabuwar fata ta Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, wadda ke da nufin rage raɗaɗin da bala’o’in jin-ƙai ke haifarwa a ƙasar. Ya bayyana cewa kayan abincin sun haɗa da buhun shinkafa, gero, wake, masara, man girki, da sauran kayan gina jiki.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamnan Jihar Kebbi, Nasiru Idris, ya yabawa Gwamnatin Tarayya kan wannan tallafi, yana mai cewa shirin zai taimaka matuƙa wajen rage wahalhalun al’ummar jihar. Ya kuma tabbatar da jajircewar gwamnatinsa wajen haɗa kai da Gwamnatin Tarayya don rage talauci, yunwa da cututtuka.

Gwamnan ya yi kira ga waɗanda suka amfana da shirin da su yi amfani da tallafin yadda ya dace, tare da tabbatar musu da ƙarin tallafi nan gaba. Haka kuma ya buƙace su da su nuna godiya ta hanyar sake zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu a wa’adi na biyu.

Rahoton Radio Nigeria ya nuna cewa wasu daga cikin waɗanda suka amfana sun yaba da ƙoƙarin gwamnatocin tarayya da jiha, inda suka tabbatar da cewa tallafin ya zo a kan lokaci kuma za su yi amfani da shi yadda ya kamata.

An kaddamar da shirin ne ta hannun gwamnan jihar tare da taimakon Ƙaramin Ministan Harkokin Jin-ƙai da Rage Talauci, a gaban manyan jami’an gwamnatocin tarayya da jiha.

COV: Sani Dutsinma

Gwamnatin Tarayya Ta Horar da Masu Shigo da Kaya da Masu Ruwa da Tsaki kan Kasuwanci

Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada aniyarta ta ƙarfafa ƙa’idojin ɗa’a a harkar shigo da kaya a matsayin wani muhimmin mataki na ƙara kuɗaɗen shiga da bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa.

Babban Sakataren Ma’aikatar Kuɗi ta Tarayya, Mista Raymond Omenka, ne ya bayyana hakan a yayin wani taron wayar da kai na kwana guda ga masu shigo da kaya, hukumomin da ke da alhaki da sauran masu ruwa da tsaki. Taron ya gudana a Kano, mai taken “Ɗa’a a Harkar Shigo da Kaya don Inganta Tara Kuɗaɗen Shiga.”

Sakataren Dindindin ya bayyana cewa ɓangaren shigo da kaya muhimmin ginshiƙi ne a tattalin arziƙin ƙasa, inda ya ce yana taka rawar gani wajen samar da kayayyaki da ayyuka, ƙirƙirar guraben ayyukan yi, da sauƙaƙa hulɗar kasuwanci da ƙasashen waje.

Da take wakiltarsa, Mataimakiyar Darakta a Sashen Hulɗar Kasuwanci, Rukayyatu Abdullahi, ta ce damar da ke akwai na ƙara kuɗaɗen shiga ta hanyar bin ƙa’idojin ɗa’a a ɓangaren shigo da kaya babba ce ƙwarai. Ta jaddada cewa aiki da gaskiya da riƙon amana na samar da daidaito da adalci ga dukkan masu shigo da kaya.

A nasa jawabin babban bako, Daraktan Sashen Kasuwanci da Musayar Kuɗaɗe na Babban Bankin Nijeriya (CBN), Dakta Musa Nakoji, wanda Jamilu Ado ya wakilta, ya ce taron zai bai wa masu ruwa da tsaki damar amfani da ƙa’idojin ɗa’a a harkar shigo da kaya a fannoni daban-daban na kasuwanci da rayuwar ɗan Adam, wanda hakan zai ƙara ingancin tattalin arziƙi.

Daga cikin muhimman abubuwan da suka gudana a taron akwai gabatar da takardu daga Hukumar Kwastam ta Nijeriya, Hukumar Kula da Inganci ta Nijeriya (SON), Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), da Ƙungiyar Masu Shigo da Kaya ta Nijeriya.

Fiye da mahalarta 151 ne suka halarci taron.

ABDULLAHI JALALUDDEEN, KANO

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara