Labarai
Gwamnatin Kano ta Samar da Babura Don Inganta Yaki da Cutar Tarin Fuka a Karkara
Daga Abdullahi Jalaluddeen
Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da jerin babura domin kara inganta gwajin cutar tarin fuka (TB) a yankunan karkara, a wani mataki na kokarin dakile yaduwar cutar.
Kwamishinan Lafiya na jihar, Dakta Abubakar Labaran Yusuf, ne ya bayyana hakan yayin wani taro na bikin Ranar Yaki da Tarin Fuka ta Duniya, wadda ake gudanarwa a duk shekara a ranar 24 ga watan Maris.
Ya ce an tsara wannan shiri ne domin kai ayyukan gwaji kai tsaye zuwa yankunan da ke da wahalar isa.
A cewarsa, a halin yanzu Kano na da cibiyoyin gwaji da kula da tarin fuka guda 1,391 a fadin kananan hukumomi 44 na jihar.

Ya bayyana cewa sabbin baburan da aka kaddamar za su taimaka wajen cike gibin da ke akwai wajen samun damar kai ayyukan lafiya, musamman a yankunan karkara da ke nesa da cibiyoyin kiwon lafiya ko kuma inda ake fuskantar kalubalen kai dauki cikin gaggawa.
Ya jaddada cewa maganin tarin fuka, kyauta ne ga marasa lafiya tsawon watanni shida na jinya, daidai da manufar gwamnatin jihar kan yaki da cutar.
Dakta Yusuf ya kara da cewa jihar na ci gaba da samun gagarumin ci gaba wajen rage yawaitar tarin fuka da sauran cututtuka masu yaduwa da ke barazana ga lafiyar al’umma.
Kwamishinan ya sake tabbatar da kudirin gwamnati na kara karfafa tsarin sa ido kan cututtuka da kuma fadada samun muhimman ayyukan kiwon lafiya a fadin Jihar Kano.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
