Connect with us

Labarai

Kebbi: An Samu Asarar Rayuka a Rikicin Alwasa

Published

on

Daga Sani Dutsinma

Rundunar ‘Yan Sanda a Jihar Kebbi ta ce an dawo da zaman lafiya a ƙauyen Alwasa da ke Ƙaramar Hukumar Argungu.

Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, SP Bashir Usman, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

Ya ce ƙauyen Alwasa na cikin kulawar tsaro, biyo bayan gaggauta tura jami’an ‘yan sanda tare da ƙarin dakaru, waɗanda ke kan aiki domin sa ido kan yanayin tsaro, tabbatar da doka da oda, da kuma hana sake ɓarkewar rikici.

A cewar sanarwar, lamarin ya faru ne a lokacin bikin Sallah, inda rikici ya ɓarke tsakanin wasu matasa, wanda ya yi sanadiyyar asarar rayuka, yayin da wasu suka  jikkata, wadanda a halin yanzu suke samun kulawa a Asibitin Gwamnati na Argungu.

Bayan wannan, an samu harin ramuwar gayya wanda ya haifar da ƙarin asarar rayuka. Rundunar ‘yan sandan ta ce ta fara gudanar da cikakken bincike kan lamarin, tare da ƙoƙarin gano da kama duk waɗanda ke da hannu a ciki.

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, CP Umar Mohammed Hadejia, ya yi Allah-wadai da lamarin, tare da gargadin cewa duk wanda aka samu da hannu cikin aikata laifi ko tayar da tarzoma zai fuskanci fushin hukunma.

Ya kuma buƙaci mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu, su guji yaɗa jita-jita, su kuma kauce wa ɗaukar doka a hannunsu, yana mai cewa za a ci gaba da sanar da jama’a.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara