Labarai
Kebbi: An Samu Asarar Rayuka a Rikicin Alwasa
Daga Sani Dutsinma
Rundunar ‘Yan Sanda a Jihar Kebbi ta ce an dawo da zaman lafiya a ƙauyen Alwasa da ke Ƙaramar Hukumar Argungu.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, SP Bashir Usman, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.
Ya ce ƙauyen Alwasa na cikin kulawar tsaro, biyo bayan gaggauta tura jami’an ‘yan sanda tare da ƙarin dakaru, waɗanda ke kan aiki domin sa ido kan yanayin tsaro, tabbatar da doka da oda, da kuma hana sake ɓarkewar rikici.
A cewar sanarwar, lamarin ya faru ne a lokacin bikin Sallah, inda rikici ya ɓarke tsakanin wasu matasa, wanda ya yi sanadiyyar asarar rayuka, yayin da wasu suka jikkata, wadanda a halin yanzu suke samun kulawa a Asibitin Gwamnati na Argungu.
Bayan wannan, an samu harin ramuwar gayya wanda ya haifar da ƙarin asarar rayuka. Rundunar ‘yan sandan ta ce ta fara gudanar da cikakken bincike kan lamarin, tare da ƙoƙarin gano da kama duk waɗanda ke da hannu a ciki.
Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, CP Umar Mohammed Hadejia, ya yi Allah-wadai da lamarin, tare da gargadin cewa duk wanda aka samu da hannu cikin aikata laifi ko tayar da tarzoma zai fuskanci fushin hukunma.
Ya kuma buƙaci mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu, su guji yaɗa jita-jita, su kuma kauce wa ɗaukar doka a hannunsu, yana mai cewa za a ci gaba da sanar da jama’a.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
