Labarai
Hajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
Daga Usman Muhammad Zaria
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa tace ta dawo da ci gaba da bitar maniyyatan aikin hajjin bana a dukkan kananan hukumomin jihar bayan kammala azumin watan Ramadan.
Daraktan Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala ganawa da manyan jami’an hukumar a Dutse babban birnin jihar.
Yana mai cewar, hukumar da dakatar da bitar ne saboda azumin watan ramadan.
A don haka, a zancen da ake yi yanzu, an dawo da bitar maniyyatan gadan-gadan domin kara fadakar da su gami da ilmantar da su yadda za su gudanar da aikin hajji a kasa mai tsarki.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kuma bukaci maniyyata da su tashi tsaye wajen ganin sun samu ilimin aikin hajji domin samun damar yin aikin hajji karbabbe.
Yayi nuni da cewar, hukumar ta kammala shirye-shiryen tantance lafiyar maniyyata, wanda hakan ya sanya hukumar aikin hajji ta kasa ta jinjina wa tsarin jihar Jigawan, kuma ta farko wajen yin hakan.
Labbo, ya kara da cewar hukumar za ta yi zama na musamman da shugabannin shiyoyinta na jihar da kuma jami’anta na kananan hukumomi wato center officers domin tattauna muhimman batutuwa da suka shafi tsarin fara jigilar maniyatan daga nan gida zuwa ƙasa mai tsarki.
Ya kuma yabawa Gwamna Umar Namadi, bisa goyon bayan da yake ba su domin ganin jihar ta ci gaba da zama ta ɗaya a gudanar da aikin hajji.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
