Labarai
Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar 2026.
Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Dutse.
Ya bayyana cewa katin rigakafin wajibi ne ga dukkan maniyyatan da za su tafi ƙasar Saudiyya domin aikin Hajji.

Alhaji Labbo wanda ya bayyana cewa jihar Jigawa na daga cikin jihohin da suka fara kammala shirye-shiryen aikin Hajjin shekarar 2026, ya kara da cewa ana ci gaba da gudanar da tarukan wayar da kai da horar da maniyyata a kowace rana a dukkan ƙananan hukumomi 27 na jihar a cibiyoyin da aka tanadar
Ya ce nan ba da jimawa ba hukumar za ta fara raba yunifom da sauran kayayyakin tafiya ga maniyyatan 2026.

Labbo ya yaba wa ma’aikatan hukumar bisa ƙwazon su da haɗin kai wajen gudanar da ayyukansu.
Haka kuma, shugaban hukumar ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa ci gaba da ba su goyon baya da haɗin kai.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
