Connect with us

Labarai

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Published

on

Daga Khadijah Aliyu

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da suka maƙale a ƙasashen waje, waɗanda aka dawo da su daga Niamey, Jamhuriyar Nijar, a matsayin wani ɓangare na shirin dawo da ’yan ƙasa na son rai da Gwamnatin Tarayya ke gudanarwa.

An kawo waɗanda aka dawo da su cikin motoci kirar bas guda 12, inda suka isa Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano da misalin ƙarfe 5 da minti 10 na yamma, inda jami’ai suka tarbe su tare da yi musu rijista da tantancewa.

Da yake magana da manema labarai a filin jirgin saman, Shugaban Ayyuka na NEMA a ofishin Kano, Dakta Nura Abdullahi, ya ce an dawo da mutanen ne bisa son ransu, ba tare da an tilasta su ba.

Abdullahi ya bayyana cewa waɗanda aka dawo da su sun haɗa da  maza 267, da mata 101, sai yara maza 82, da yara mata 72, daga jihohi daban-daban ciki har da Kano, Jigawa, Filato da Bauchi.

Ya ƙara da cewa NEMA tare da haɗin gwiwar sauran masu ruwa da tsaki sun tanadi dukkan matakan da suka dace domin kula da waɗanda aka dawo da su bayan isowarsu.

A cewarsa, da dama daga cikin waɗanda aka dawo da su sun yi hijira ne ba bisa ƙa’ida ba, domin neman ingantacciyar rayuwa, inda suka nufi ƙasashe kamar Libya da Aljeriya, amma suka bukaci dawowa  gida bayan fuskantar ƙalubale a hanya.

Abdullahi ya kuma ce an tanadi wuraren zama na wucin gadi, tare da raba muhimman kayan agaji kamar abinci, bargo, gidan sauro, da kayan tsafta  na mata (dignity kits) ga waɗanda aka dawo da su.

Shi a nasa jawabin, wakilin Ma’aikatar Harkokin Waje ta Tarayya, Malam Magaji Umar, ya yaba wa Gwamnatin Tarayya kan sauƙaƙa dawowar ’yan ƙasar cikin aminci.

Ya ce wannan shiri ya yi daidai da manufofin ƙasa kan harkokin hijira, da kuma ƙudirin gwamnati na kare ’yan Najeriya a ƙasashen waje.

Umar ya ƙara da cewa wannan aiki ya samu nasara ne sakamakon haɗin gwiwar manyan hukumomi da suka haɗa da Ma’aikatar Harkokin Waje, ofisoshin jakadancin Najeriya, da Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira ta Duniya (IOM).

Hukumar ta NEMA  ce ta tarbi waɗanda aka dawo da su  tare da haɗin gwiwar sauran hukumomi da suka haɗa da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jiha (SEMA), Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira (NCFRMI), Kungiyar Red Cross ta Najeriya, da Hukumar Shige da Fice ta Najeriya.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara