Labarai
NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar
Daga Khadijah Aliyu
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da suka maƙale a ƙasashen waje, waɗanda aka dawo da su daga Niamey, Jamhuriyar Nijar, a matsayin wani ɓangare na shirin dawo da ’yan ƙasa na son rai da Gwamnatin Tarayya ke gudanarwa.
An kawo waɗanda aka dawo da su cikin motoci kirar bas guda 12, inda suka isa Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano da misalin ƙarfe 5 da minti 10 na yamma, inda jami’ai suka tarbe su tare da yi musu rijista da tantancewa.
Da yake magana da manema labarai a filin jirgin saman, Shugaban Ayyuka na NEMA a ofishin Kano, Dakta Nura Abdullahi, ya ce an dawo da mutanen ne bisa son ransu, ba tare da an tilasta su ba.
Abdullahi ya bayyana cewa waɗanda aka dawo da su sun haɗa da maza 267, da mata 101, sai yara maza 82, da yara mata 72, daga jihohi daban-daban ciki har da Kano, Jigawa, Filato da Bauchi.
Ya ƙara da cewa NEMA tare da haɗin gwiwar sauran masu ruwa da tsaki sun tanadi dukkan matakan da suka dace domin kula da waɗanda aka dawo da su bayan isowarsu.
A cewarsa, da dama daga cikin waɗanda aka dawo da su sun yi hijira ne ba bisa ƙa’ida ba, domin neman ingantacciyar rayuwa, inda suka nufi ƙasashe kamar Libya da Aljeriya, amma suka bukaci dawowa gida bayan fuskantar ƙalubale a hanya.
Abdullahi ya kuma ce an tanadi wuraren zama na wucin gadi, tare da raba muhimman kayan agaji kamar abinci, bargo, gidan sauro, da kayan tsafta na mata (dignity kits) ga waɗanda aka dawo da su.
Shi a nasa jawabin, wakilin Ma’aikatar Harkokin Waje ta Tarayya, Malam Magaji Umar, ya yaba wa Gwamnatin Tarayya kan sauƙaƙa dawowar ’yan ƙasar cikin aminci.
Ya ce wannan shiri ya yi daidai da manufofin ƙasa kan harkokin hijira, da kuma ƙudirin gwamnati na kare ’yan Najeriya a ƙasashen waje.
Umar ya ƙara da cewa wannan aiki ya samu nasara ne sakamakon haɗin gwiwar manyan hukumomi da suka haɗa da Ma’aikatar Harkokin Waje, ofisoshin jakadancin Najeriya, da Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira ta Duniya (IOM).
Hukumar ta NEMA ce ta tarbi waɗanda aka dawo da su tare da haɗin gwiwar sauran hukumomi da suka haɗa da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jiha (SEMA), Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira (NCFRMI), Kungiyar Red Cross ta Najeriya, da Hukumar Shige da Fice ta Najeriya.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
