Ilimi
Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu
Daga Usman Muhammad Zaria
Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a matsayin ginshiƙin ci gaban kasa.
Ya bayyana hakan ne lokacin da ya jagoranci wata tawaga domin zagayawa makarantun yankin, don duba yadda ake koyarwa da kuma hanyoyin ilmantarwa.

A cewarsa, ziyarar na daga cikin ƙoƙarinsa na inganta tsarin ilimi a ƙaramar hukumar Birnin Kudu, wanda ya yi daidai da kudurori 12 na Gwamna Umar Namadi.
Muhammad Uba ya kuma duba wasu makarantu daban-daban, inda ya tattauna da malamai da ɗalibai domin tantance ci gaba da kuma gano wuraren da ke buƙatar gyara.

Wannan ziyara ta biyo bayan wasu sabbin ci gaba a ɓangaren ilimi na ƙaramar hukumar, ciki har da bayar da sabuwar mota ga Hukumar Ilimi ta Ƙaramar Hukuma daga Gwamnatin Jihar Jigawa ta hannun Ma’aikatar Ilimin Firamare.
Shugaban ƙaramar hukumar ya kuma tabbatar da an saka sabbin tayoyi a motar, wanda ke nuna jajircewarsa wajen tallafa wa ilimi a yankin.

A nasa jawabin, shugaban hukumar Ilimin Bai Daya na jihar (SUBEB), Haruna Idris Hadejia, ya yaba wa shugaban ƙaramar hukumar bisa ƙoƙarinsa da jajircewarsa wajen bunƙasa ilimi a Birnin Kudu.
Ya bayyana Dakta Builder Muhammad a matsayin jajirtacce da ya yi fice a Jihar Jigawa, inda ya nuna yadda yake da himma wajen aiwatar da ayyukan ci gaban ilimi.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
