Labarai
Hajjin 2026: Jigawa ta Kammala Samun Biza ga Dukkan Maniyyatan Jihar
Daga Usman Muhammad Zaria
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta fara raba kayan sawa (uniform) da kayan tafiya ga maniyyatan hajjin shekarar 2026.
Shugaban Hukumar kumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga wakilin Rediyon Najeriya a Dutse, babban birnin jihar.
Ya bayyana cewa ƙaddamar da wannan shiri na rabon kayan wani ɓangare ne na shirye-shiryen gudanar da aikin hajjin bana. Yana mai cewa tuni hukumar ta fara bai wa jami’an yankuna da cibiyoyi kayan sawa da jakunkuna domin su rarraba wa maniyyata.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce, ya zuwa yanzu hukumar ta samu nasarar kammala dukkan biza na maniyyatan jihar, tare da kammala dukkan shirye-shiryen da suka dace domin sauƙaƙa jigilar maniyyatan cikin kwanciyar hankali.

Daraktan ya ce Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON ta tsara fara jigilar rukuni na farko na maniyyatan Jigawa daga Filin Jirgin Sama na Nuhu Muhammadu Sunusi da ke Dutse zuwa ƙasar Saudiyya a ranar 4 ko 5 ga watan Mayu, 2026.
Ahmed Labbo ya kuma bayyana cewa Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ta bai wa kamfanin jiragen sama na Umza Air alhakin jigilar maniyyatan Jigawa zuwa Saudiyya.
A cewarsa, nan ba da jimawa ba za a fara yi wa maniyyata allurar rigakafi a hedikwatar hukumar da sauran cibiyoyin da aka tanada a fadin jihar.
Shugaban hukumar ya buƙaci maniyyata su kasance masu halartar darussan horaswa a ae yi a kullum, tare da zama jakadu nagari ga jihar da ƙasa baki ɗaya.

Ya kara da cewa jami’an hukumar, hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki za su fara zagayen cibiyoyin horaswa domin wayar da kan maniyyata kan matakan tsaro, lafiya da tsafta yayin zaman su a sansani da kuma a ƙasa mai tsarki.
A ƙarshe, ya yaba wa Gwamna Umar Namadi da dukkan masu ruwa da tsaki bisa goyon baya da haɗin kai da suke bai wa hukumar domin gudanar da aiki cikin nasara ba tare da wata tangarda ba.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
