Connect with us

Labarai

Hajjin 2026: Jigawa ta Kammala Samun Biza ga Dukkan Maniyyatan Jihar

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta fara raba kayan sawa (uniform) da kayan tafiya ga maniyyatan hajjin shekarar 2026.

Shugaban Hukumar kumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga wakilin Rediyon Najeriya a Dutse, babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa ƙaddamar da wannan shiri na rabon kayan wani ɓangare ne na shirye-shiryen gudanar da aikin hajjin bana. Yana mai cewa tuni hukumar ta fara bai wa jami’an yankuna da cibiyoyi kayan sawa da jakunkuna domin su rarraba wa maniyyata.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce, ya zuwa yanzu hukumar ta samu nasarar kammala dukkan biza na maniyyatan jihar, tare da kammala dukkan shirye-shiryen da suka dace domin sauƙaƙa jigilar maniyyatan cikin kwanciyar hankali.

Daraktan ya ce Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON ta tsara fara jigilar rukuni na farko na maniyyatan Jigawa daga Filin Jirgin Sama na Nuhu Muhammadu Sunusi da ke Dutse zuwa ƙasar Saudiyya a ranar 4 ko 5 ga watan Mayu, 2026.

Ahmed Labbo ya kuma bayyana cewa Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ta bai wa kamfanin jiragen sama na Umza Air alhakin jigilar maniyyatan Jigawa zuwa Saudiyya.

A cewarsa, nan ba da jimawa ba za a fara yi wa maniyyata allurar rigakafi a hedikwatar hukumar da sauran cibiyoyin da aka tanada a fadin jihar.

Shugaban hukumar ya buƙaci maniyyata su kasance masu halartar darussan horaswa a ae yi a kullum, tare da zama jakadu nagari ga jihar da ƙasa baki ɗaya.

Ya kara da cewa jami’an hukumar, hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki za su fara zagayen cibiyoyin horaswa domin wayar da kan maniyyata kan matakan tsaro, lafiya da tsafta yayin zaman su a sansani da kuma a ƙasa mai tsarki.

A ƙarshe, ya yaba wa Gwamna Umar Namadi da dukkan masu ruwa da tsaki bisa goyon baya da haɗin kai da suke bai wa hukumar domin gudanar da aiki cikin nasara ba tare da wata tangarda ba.

 

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara