Labarai
Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya
Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin Musulunci da ci gaban jihar ba.
Kwamishinan Harkokin Addini, Muhammad Sani Aliyu, ya bayyana haka yayin wani taron manema labarai a Birnin Kebbi. Ya ce zargin ba shi da tushe, kuma ya biyo bayan wata hudubar Juma’a da Bashir Jega ya yi inda ya soki gwamnati kan harkokin addini.
A cewarsa, daga cikin manyan nasarorin gwamnatin akwai kafa Ma’aikatar Harkokin Addini, wadda ya ce al’ummar jihar suka dade suna fata sama da shekaru 25 ba tare da an cimma ba.
Ya kuma ce gwamnati ta kara karfafa hukumomi kamar Hukumar Zakka da Waqafi, da Hukumar Wa’azi, da kuma Hukumar Hisbah, tare da samar musu dokoki da tallafi domin gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.
Kwamishinan ya bukaci malaman addini su mai da hankali wajen wa’azin zaman lafiya da hadin kai, tare da kauce wa shiga rigingimun siyasa da ka iya yaudarar al’umma.
Sani Haruna/Kebbi
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoƊaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano
