Labarai
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Dauki Matakan Kawar Da Nama Me Guba A Kasuwannin Jihar
Gwamnatin jihar Kwara ta ce ta samar da matakan kare lafiyar jama’a a daidai lokacin da ake ta yayata jita-jitar sayar da naman Sa me guba a wasu kasuwannin jihar.
A cikin wata sanarwa da kwamishinar lafiya ta jihar, Dr. Amina Ahmed El-Imam ta fitar, ta ce an kafa wata babbar tawaga don sanya ido kan lamarin.
Sanarwar ta bayyana cewa, gwamnatin jihar ta kwace dukkan naman da ake zargi domin yin gwaji akan su, bayan wata ganawa da aka yi da masu ruwa da tsaki naKasuwar.
Sanarwar ta bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu, yayin da ake ci gaba da bincike don tabbatar da gaskiyar lamarin.
Sanarwar ta kuma yabawa shugabannin kasuwar bisa hadin kan da suka bayar don shawo kan lamarin.
Sama da shanu talatin da uku 33 ake zargin sun mutu sakamakon guba a yankin Atere da ke Ilọrin.
An kuma yi zargin cewa an yanka matattun dabbobin ne aka raba wa mahauta domin sayarwa a kasuwanni.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
