Connect with us

Labarai

Gwamna Kefas ya ziyarci Takum Inda guguwa ta lalata gidaje sama da 100 a Taraba

Published

on

Gwamna Agbu Kefas na jihar Taraba ya tabbatar wa mazauna garin Takum cewa gwamnati za ta nemo hanyoyin tallafawa don sake gina gidajen da guguwa ta lalata a yammacin ranar Talata.

 

Wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai ya raba wa manema labarai, ta ce Kefas ya bayar da wannan tabbacin ne a ranar Laraba a ziyarar da ya kai yankin.

 

Idan ba a manta ba a ranar Talatar da ta gabata ce ruwan sama kamar da bakin kwarya ya lalata gidaje da dama, lamarin da ya sa mazauna yankin da dama suka rasa matsuguni.

 

Sanarwar ta ci gaba da cewa, Dr. Kefas ya fara tura tawagar jami’an jihar zuwa Takum domin tantance barnar da aka yi.

 

Daga bisani kuma Gwamna Kefas ya ziyarci Takum domin gani da idon sairin barnar da iskan ya yi.

 

Yayin zagaya wasu yankunan da abin ya shafa na birnin, gwamnan ya jajanta wa wadanda abin ya shafa tare da gabatar da kalaman karfafa gwiwa.

 

Bugu da kari, gwamnan ya gana da shugabannin al’umma da mazauna yankin, ya ba su tabbacin gwamnati a shirye suke na tallafawa wajen sake gina gidajensu da suka lalace.

 

Mazauna garin Takum da suka fito kan tituna domin tarbar gwamnan, sun bayyana jin dadinsu da daukar matakin da ya dace cikin gaggawa.

 

Sani Sulaiman/Wababe

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara