Connect with us

Labarai

Manyan Alkalai Sun Bukaci Birtaniya Ta Daina Siyar wa Isra’ila Makamai

Published

on

Tsofaffin alƙalan kotun ƙoli sun bi sahun masana shari’a fiye da 600 wajen kira ga gwamnatin Birtaniya ta daina sayar wa Isra’ila makamai.

Cikin wata takarda zuwa ga firaiminista Rishi Sunak, tsofaffin alƙalan sun ce dole ne a kawo ƙarshen fitar da makamai saboda Birtaniya na cikin haɗarin karya dokokin duniya.

Tuni dai mista Sunak yake fuskantar matsin lamba bayan sojojin Isra’ila sun kashe wasu ma’aikatan agaji bakwai.

A ranar Talata ne, firaiministan ya ce Birtaniya tana da wani tsari na kaffa-kaffa game da lasisin makamai.

Tsohuwar shugabar kotun ƙoli, Lady Hale na cikin masana sama da 600 da suka sa hannu kan takardar mai shafuka 17.

Takardar ta ce akwai buƙatar a ɗauki mataki na gaske domin hana Birtaniya faɗawa matsalar karya dokokin ƙasa da ƙasa har da yiwuwar saɓa yarjejeniyar da ta shafi dokokin kisan kiyashi.

Sauran mutanen da suka sa hannu kan takardar sun haɗa da tsofaffin alƙalan kotun ƙoli Lord Sumption da Lord Wilson tare da wasu alƙalai tara da manyan lauyoyi 69.

Labarai

Labarai3 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai3 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai16 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara