Labaran Ketare
Isra’ila na ci gaba da ruwan wuta a Gaza duk da shigowar Ramadan
Falasɗinawa sun fara azumin Ramadan yayin da ake ci gaba da gwabza faɗa a yankin tsakanin dakarun Isra’ila da sojojin Hamas kuma babu wata alamar cewa za a cimma tsagaita wuta.
Isra’ila ta lalata muhallan akasarin al’ummar Gaza, yayin da a alokaci guda hukumomin bayar da agaji ke gargaɗin cewa mutane za su mutu saboda yunwa.
A daren da ya gabata an yi artabu bayan da ƴansandan Isra’ila suka hana ɗarurtuwan matasa Falasɗinawa shiga masallacin Al Aqsa.
Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu dai ya sha alwashin ci gaba da ruwan wuta a birnin Rafah da ke kudancin Gaza duk da gargaɗin da shugaban Amurka Joe Biden ya yi kan batun.
A cikin saƙonsa na Ramadan ga al’ummar Gaza, Biden ya ce Musulmai da dama a duniya za su yi azumi ne da Falasɗinawa a ransu.
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai6 days ago
An Kashe Makiyaya 2 Da Shanu 150 A Sabon Hari A Filato