Fasaha
Abdulsalami ya shawarci Kasashen Nijar, Mali, Burkina Faso su koma ECOWAS
Tsohon shugaban Kasa, kuma ɗaya daga cikin masu shiga tsakani kan rikicin ƙungiyar ECOWAS da jumhuriyar Nijar, Janar Abdulsalami Abubakar mai ritaya, ya yi kira ga ƙasashen yanki uku da su koma cikin ƙungiyar.
Wannan ne karon farko da mai shiga tsakanin ya furta cewa, ficewar Ƙasashen Burkina-Faso da Mali da kuma jumhuriya Nijar daga ECOWAS mayar da hannun agogo baya ne.
A cewarsa matakin ƙasashen zai iya kawo naƙasu ga tattalin arzikin yankin.
Janar Abdulsalami Abubakar ya yi kira ga ƙasashen uku da su dawo cikin garke a yi tafiya da su, domin sarkin yawa ya fi sarkin ƙarfi.
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai7 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Labarai7 hours ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Ilimi4 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha1 day ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Kasuwanci1 day ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati
-
Fasaha1 day ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet