Labarai
An jikkata Yan jarida bakwai a wani hari a Gaza
Akalla ƴan jarida bakwai ne suka jikkata sakamakon hari ta sama da Isra’ila ta kai asibiti a tsakiyar Gaza.
Rundunar sojin Isra’ila ta ce ta kai wa cibiyar bayar da umarni ta masu ikirarin jihadi da ke harabar asibitin al-Aqsa hari, inda ɗaruruwan mutane ke fake wa.
Mutane huɗu sun rasa rayukansu, ciki har da wani mutum guda da Isra’ila ta bayyana a matsayin kwamandan mayakan Jihadi.
A wani sabon labarin kuma, sojin Isra’ilan sun baje kolin makaman da suka ce sojojinsu sun kama a wani samame da suka kai asibitin al-Shifa da ke birnin Gaza, bayan zargin mayakan Hamas da ɓuya a cibiyoyin lafiya.
Jami’an lafiya a Falasɗinu sun ce mutane tara ne suka rasa rayukansu a harin da Isra’ila ta kai a Bani Suhaila da ke makwabtaka da Khan younis.
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha3 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai16 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci3 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Ilimi3 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert
-
Labarai2 hours ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka