Labarai
Gwamna Kefas ya ziyarci Takum Inda guguwa ta lalata gidaje sama da 100 a Taraba
Gwamna Agbu Kefas na jihar Taraba ya tabbatar wa mazauna garin Takum cewa gwamnati za ta nemo hanyoyin tallafawa don sake gina gidajen da guguwa ta lalata a yammacin ranar Talata.
Wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai ya raba wa manema labarai, ta ce Kefas ya bayar da wannan tabbacin ne a ranar Laraba a ziyarar da ya kai yankin.
Idan ba a manta ba a ranar Talatar da ta gabata ce ruwan sama kamar da bakin kwarya ya lalata gidaje da dama, lamarin da ya sa mazauna yankin da dama suka rasa matsuguni.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, Dr. Kefas ya fara tura tawagar jami’an jihar zuwa Takum domin tantance barnar da aka yi.
Daga bisani kuma Gwamna Kefas ya ziyarci Takum domin gani da idon sairin barnar da iskan ya yi.
Yayin zagaya wasu yankunan da abin ya shafa na birnin, gwamnan ya jajanta wa wadanda abin ya shafa tare da gabatar da kalaman karfafa gwiwa.
Bugu da kari, gwamnan ya gana da shugabannin al’umma da mazauna yankin, ya ba su tabbacin gwamnati a shirye suke na tallafawa wajen sake gina gidajensu da suka lalace.
Mazauna garin Takum da suka fito kan tituna domin tarbar gwamnan, sun bayyana jin dadinsu da daukar matakin da ya dace cikin gaggawa.
Sani Sulaiman/Wababe
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha4 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai1 day ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Labarai15 hours ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Kasuwanci4 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi7 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Ilimi4 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert