Connect with us

Labarai

Gwamna Kefas ya ziyarci Takum Inda guguwa ta lalata gidaje sama da 100 a Taraba

Published

on

Gwamna Agbu Kefas na jihar Taraba ya tabbatar wa mazauna garin Takum cewa gwamnati za ta nemo hanyoyin tallafawa don sake gina gidajen da guguwa ta lalata a yammacin ranar Talata.

 

Wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai ya raba wa manema labarai, ta ce Kefas ya bayar da wannan tabbacin ne a ranar Laraba a ziyarar da ya kai yankin.

 

Idan ba a manta ba a ranar Talatar da ta gabata ce ruwan sama kamar da bakin kwarya ya lalata gidaje da dama, lamarin da ya sa mazauna yankin da dama suka rasa matsuguni.

 

Sanarwar ta ci gaba da cewa, Dr. Kefas ya fara tura tawagar jami’an jihar zuwa Takum domin tantance barnar da aka yi.

 

Daga bisani kuma Gwamna Kefas ya ziyarci Takum domin gani da idon sairin barnar da iskan ya yi.

 

Yayin zagaya wasu yankunan da abin ya shafa na birnin, gwamnan ya jajanta wa wadanda abin ya shafa tare da gabatar da kalaman karfafa gwiwa.

 

Bugu da kari, gwamnan ya gana da shugabannin al’umma da mazauna yankin, ya ba su tabbacin gwamnati a shirye suke na tallafawa wajen sake gina gidajensu da suka lalace.

 

Mazauna garin Takum da suka fito kan tituna domin tarbar gwamnan, sun bayyana jin dadinsu da daukar matakin da ya dace cikin gaggawa.

 

Sani Sulaiman/Wababe

Labarai

Labarai15 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai16 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai1 day ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha4 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci4 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi4 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi7 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara