Labarai
ECOWAS Za Ta Kashe Dala Miliyan 25 Don Yaki Da Ta’addanci A Najeriya Da Nijar
Kungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen Afirka ta Yamma ECOWAS ta ware Dala miliyan 25 da zimmar yaƙi da ta’addanci a ƙasashen Najeriya, da Nijar, da Mali, da Burkina Faso.
Ecowas ta tsara kashe kuɗin ne a shekarar 2024, kamar yadda Kwamashinar Raya Al’umma ta ECOWAS Farfesa Fatou Sarr ta bayyana a hedikwatar ƙungiyar da ke Abuja yau Juma’a.
Farfesar ta ce an ware miliyan huɗu daga cikin kuɗin don ayyukan agaji musamman ga mutanen da bala’o’i suka shafa.
“Haka nan, ECOWAS ta ware dala miliyan ɗaya da zimmar daidaita rayuwar mutanen da ta’addanci ya shafa, kamar ‘yan gudun hijira da kuma waɗanda aka ji wa rauni,” inji ta.
Ta ƙara da cewa a 2023 kaɗai, ECOWAS ta ba da tallafin Dala miliyan goma sha biyu da dubu dari shida ga mutane sama da miliyan huɗu da ta’addanci ya shafa a yammacin Afirka.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
