Connect with us

Labarai

Dokar Auren Jinsi: Majalisar Ghana Ta Fusata Da Matakin Nana Akufo Addo

Published

on

Kakakin Majalisar Ghana ya ki amincewa da sahale nadin wasu sabbin ministoci bisa kafa hujja da cewa har sai shugaban kasar Nana Akufo-Addo ya sanya hannu a dokar haramta auren jinsi da Majalisar ta kada kuri’ar amincewa da ita a watan jiya, amma har zuwa yanzu shugaban ya gaza sanya hannu.

Ana dai ganin shugaba Nana Akufo-Addo na jan kafa wajen rattaba hannu kan kudirin don mayar da shi doka ne sakamakon kakkausar sukar da kudirin ke fuskanta daga kungiyoyin kare hakkin dan adam musamman daga kasashen Turai.

 

Kafin wannan mataki na Majalisar dai, shugaba Addo ya ce yana jiran hukuncin kotun kolin kasar gabanin rattaba hannu kan dokar, bayan da masu fafutukar tabbatar da auren na jinsi suka daukaka kara kan matakin.

 

Wasu alkaluma da aka tattara na nuna cewa galibin al’ummar Ghana na goyon bayan haramta auren na jinsi da kuma tanadin hukunci mai tsauri kan wadanda aka samu da aikatawa ko kuma da goyon baya koma tallata shi.

 

Sai dai wasu bayanai na cewa, shugaba Akufo-Addo ya samu gargadi ne daga kasashen duniya da hukumomin bayar da lamuni da ke neman lallai kar ya sanya hannu a kudirin don mayar da shi dokar.

Ghana dai ba ita ce kasar farko da ke fuskantar matsala wajen aiwatar da wannan doka ta haramta auren jinsi ba, domin kuwa makamancin lamarin da ke faruwa a Kenya kenan, inda har zuwa yanzu kungiyoyin addinai ke ci gaba da gangami don kalubalantar mahukunta.

Labarai

Labarai7 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara