Connect with us

Ilimi

Daliban Jami’ar Nasarawa 3 Sun Mutu A Tirmitsitsin Rabon Tallafi

Published

on

Daliban Jami’ar Jihar Nasarawa 3 ne ake fargabar sun mutu  sakamakon turmutsitsin da ya faru a lokacin rabon tallafin shinkafa da gwamnatin jihar ta bada a yau Juma’a a garin Keffi.

Lamarin ya faru ne a dandalin taro na makarantar inda aka ajiye buhunan shinkafa ana jiran isowar gwamna Abdullahi Sule domin fara rabon kayayyakin.

A cewar wani dalibin da lamarin ya faru a gaban idonsa, Moses Ajah, ya ce gungun daliban da ke dakon shiga dandalin sun ci karfin jami’an tsaro tare kutsawa dandalin taron.

Ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici matuka.

Ya ce wasu dalibai  sun kwashi buhunan shinkafan suka gudu da su  duk da cewa Gwamnan bai kai ga  iiowa wurin ba domin kaddamar da rabon.

Ya  zuwa lokacin hada wannan rahoto, an ga jami’an ‘yan sanda suna bin daliban dakunan kwanansu don kwato buhunan shinkafar da suka yi awan gaba da su.

Da aka tuntubi jami’in yada labarai da kula da jami’ar, Mista Abraham Ekpo, ya ce yana sane da lamarin amma har yanzu bai samu cikakken bayani a kai ba.

Aliyu Muraki

 

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara