Ilimi
Daliban Jami’ar Nasarawa 3 Sun Mutu A Tirmitsitsin Rabon Tallafi
Daliban Jami’ar Jihar Nasarawa 3 ne ake fargabar sun mutu sakamakon turmutsitsin da ya faru a lokacin rabon tallafin shinkafa da gwamnatin jihar ta bada a yau Juma’a a garin Keffi.
Lamarin ya faru ne a dandalin taro na makarantar inda aka ajiye buhunan shinkafa ana jiran isowar gwamna Abdullahi Sule domin fara rabon kayayyakin.
A cewar wani dalibin da lamarin ya faru a gaban idonsa, Moses Ajah, ya ce gungun daliban da ke dakon shiga dandalin sun ci karfin jami’an tsaro tare kutsawa dandalin taron.
Ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici matuka.
Ya ce wasu dalibai sun kwashi buhunan shinkafan suka gudu da su duk da cewa Gwamnan bai kai ga iiowa wurin ba domin kaddamar da rabon.
Ya zuwa lokacin hada wannan rahoto, an ga jami’an ‘yan sanda suna bin daliban dakunan kwanansu don kwato buhunan shinkafar da suka yi awan gaba da su.
Da aka tuntubi jami’in yada labarai da kula da jami’ar, Mista Abraham Ekpo, ya ce yana sane da lamarin amma har yanzu bai samu cikakken bayani a kai ba.
Aliyu Muraki
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai5 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar