Connect with us

Ilimi

Daliban Makarantar Kuriga Sun Shaki Iskar ‘Yanci – Uba Sani

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da sakin yara ‘yan makaranta  dari biyu da tamanin da bakwai 287 da aka yi garkuwa da su daga Kuriga da ke karamar hukumar Chikun ta jihar

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun gwamnan jihar Uba Sani.

 

Sanarwar ta ce “Ina so in sanar da cewa an sako yaranmu na makarantar Kuriga, muna godiya ta musamman ga mai girma shugaban mu, Bola Ahmed Tinubu, bisa ba da fifiko ga tsaro da tsaron ‘yan Nijeriya, musamman kokarin da ya yi na ganin an sako ‘ya’yan makarantar Kuriga da aka sace ba tare da wani lamuni ba”.

Gwamnan ya kuma yaba da jajircewar hafsoshin sojojin Najeriya na ganin an samu nasarar sako yaran.

 

Muna kuma gode wa daukacin ‘yan Najeriya bisa addu’in da suka yi na ganin  Allah Ya dawo da yaran cikin koshin lafiya, lallai wannan ranar farin ciki ce. Muna godiya ga Allah Madaukakin Sarki.”

 

Idan dai za a iya tunawa, a ranar 7 ga watan Maris, 2024, ‘yan bindiga suka sace ‘yan makarantar firamare  da na  Sakandaren Gwamnati da ke Kuriga, inda suka kai su dajin.

 

Masu garkuwa da mutanen sun bukaci a bada kudin fansa na Nera milyan dubu daya, yayin da suka ba da wa’adin ranar 27 ga Maris, 2024, don biyan kudin.

 

Aminu Dalhatu

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara