Ilimi
Daliban Makarantar Kuriga Sun Shaki Iskar ‘Yanci – Uba Sani
Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da sakin yara ‘yan makaranta dari biyu da tamanin da bakwai 287 da aka yi garkuwa da su daga Kuriga da ke karamar hukumar Chikun ta jihar
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun gwamnan jihar Uba Sani.
Sanarwar ta ce “Ina so in sanar da cewa an sako yaranmu na makarantar Kuriga, muna godiya ta musamman ga mai girma shugaban mu, Bola Ahmed Tinubu, bisa ba da fifiko ga tsaro da tsaron ‘yan Nijeriya, musamman kokarin da ya yi na ganin an sako ‘ya’yan makarantar Kuriga da aka sace ba tare da wani lamuni ba”.

Gwamnan ya kuma yaba da jajircewar hafsoshin sojojin Najeriya na ganin an samu nasarar sako yaran.
“Muna kuma gode wa daukacin ‘yan Najeriya bisa addu’in da suka yi na ganin Allah Ya dawo da yaran cikin koshin lafiya, lallai wannan ranar farin ciki ce. Muna godiya ga Allah Madaukakin Sarki.”
Idan dai za a iya tunawa, a ranar 7 ga watan Maris, 2024, ‘yan bindiga suka sace ‘yan makarantar firamare da na Sakandaren Gwamnati da ke Kuriga, inda suka kai su dajin.
Masu garkuwa da mutanen sun bukaci a bada kudin fansa na Nera milyan dubu daya, yayin da suka ba da wa’adin ranar 27 ga Maris, 2024, don biyan kudin.
Aminu Dalhatu
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik



