Connect with us

Labarai

Dakarun Isra’ila sun lakaɗa wa likitoci duka a Gaza

Published

on

Falasɗinawa ma’aikatan lafiya a Gaza sun shaida wa BBC cewa dakarun Isra’ila sun rufe musu idanu da kyallaye, an tsare su kuma an tilasta musu tuɓe kayansu, yayin da aka yi ta lakaɗa musu duka a lokacin da sojin suka kai samame asibitin da suke aiki a watan Fabrairun da ya wuce.

Ahmed Abu Sabha, wani likita ne a asibitin Nasser, ya bayyana yadda sojin Isra’ilan suka tsare shi na tsawon mako guda, aka cinna mishi karnunka kuma suka karya masa hannu.

Abin da ya faru gare shi ya zo daidai da wasu likitocin biyu waɗanda suka nemi a sakaya sunayensu saboda tsoron ɗaukar matakan ramuwar gayya a kansu.

Sun shaida wa BBC cewa an muzanta su sun dake su, sun kwara musu ruwan sanyi kuma sun sanya su tsuguno mara daɗi na tsawon lokaci.

Haka kuma sun ce an tsare su na tsawon kwanaki kafin a sake su.

BBC ta bayyana wa ma’aikatar tsaron Isra’ila zarge-zargensu, amma bata mayar da martani kai tsaye kan tambayoyin da aka yi mata ba game da abubuwan da suka ce an yi musu, haka zalika bata musanta azaftarwar ba a ɗaiɗai kunsu, amma ta musanta cutar da wani jami’in lafiya a yaƙin da take yi.

Sun ce “duk wani cin zarafi na waɗanda ake tsare da su ya saɓawa umarnin ma’aikatar tsaron ta IDF, kuma don haka an haramta hakan”.

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara