Kasuwanci
CBN Ya Umarci ’Yan Canji Su Sake Rajista
Babban Bankin Najeriya (CBN) ya bukaci ɗaukacin ’yan canjin kuɗaɗen ƙasashen ƙetare su sake rajista domin ci gaba da harkokinsu.
Babban bankin ya bayar da wannan umarni ne a wata takarda da Daraktan Sashen tsare-tsaren harkokin kudi na bankin, Haruna Mustafa ya fitar a ranar Laraba.
“Ana umartar ’yan canjin su cika sharuddan babban bankin na mallakar lasisin u cikin watanni shida.
“Sannan, duk ’yan canjin su sani cewa suna da damar neman kowane irin lasisi kamar yadda doka ta tanadar,” in ji sanarwar.
Bankin ya kuma yi wasu sauye-sauye a tsarin gudanar da hada-hadar canji.
Daya daga ciki shi ne soke biyan kudin kafin alkalami na tilas har na Naira miliyan 200 ga masu lasisin mai daraja ta daya.
Haka kuma, bankin kolin ya kuma soke biyan kudin kafin alkalami na dole na Naira miliyan 50 ga masu rike da lasisin mai daraja ta biyu.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
