Connect with us

Ilimi

Bukin Sallah: Mai Martaba Sarkin Kauru Ya Bukaci A Ba Mata Dama Su Nemi Ilimi

Published

on

Mai martaba Sarkin Kauru ta jihar Kaduna Alhaji Zakari Ya’u Usman ya bukaci jama’ ar yankin su hada kai suyi aiki tare don dakile matsalar tsaron da yankin ke fuskanta a yanzu.

A sakon sa na barka da sallah a fadarsa da ke Kauru, Mai Martaba Sarki ya nuna matukar famuwarsa akan matslaar masu garkuwa da mutane da ke kara habaka da satar amfani gona da wasu ayukkan badala a wannan yankin.

Alhaji Zakari Ya’u ya zayyano irin kalubalen da wannan matsalar ke haifarwa tsakanin al’umma tare da kira da kakkausar murya na a dauki matakin maganinta gaba daya.

Ya Kuma bayyana irin mahimmancin hadin kan al’umma akan wannan don kawo karshensa sannan ya umurci dukkanin masu rike da sarautu suyi aiki da mutanensu tare da jami’an tsaro don samo hanyar dikile wannan muguwar ta’ada.

Mai Martaba Ya’u na II yace akwai bukatar hada karfi da karfe wajen Kare rayuka da dukiyoyi da kuma fitar da al’umma daga wannan sabuwar matsala.

Bugu da kari Banda maganar tsaro, mai martaba ya kuma tabo tare da bayyana muhimmamcin kula da ilimin ‘ya’ya mata tare da Kiran a kara basu dama suje makaranta.

Sarkin Kauru Zakari Ya’u Usman II da Malam Yusuf Zubairu (Tambarin Kauru)

Sannan yayi bayanin cewa gudummuwar da ilini ke bayarwa wajen ba jama’a damar dogara DA Kai da Kuma habakar tattalin arzikin da ci gaba.

Sannam mai Martaban bai tsaya nan ba sai da kawo irin mahimmancin da zaman lafiya da kwanciyar hankali da samarawa mabanbantan al’umma don haka ya bukaci a hada kai ayi aikin bunkasa yankin Kauru.

Ya Kuma jawo hankalin al’ummarsa game da mahimmancin zuwa asibiti don duba lafiya.

Radio Nigeria kaduna ya bada labarin cewa sakon mai martaba na sallah karama ya nuna irin yunkurin da yake wajen maganin matsalolin da jama’ar masarautar ke fuskanta, inda ya bayyana aiki tare ta bangaren ilimi, zaman lafiya da harkokin kula da lafiya a matsayin jigon ci gaban da ake bukata.

Sakataren masarautar Kauru, Mal Muhammad Sani Suleiman, (Dan’s buran Kauru)

 

Hakama Sakataren masarautar Kauru Malam Muhammad Sani Suleiman (Dan Buran Kauru) ya mika sakonsa na taya murna ga mi martaba Sarki Kauru game da cikar sa shekara 3 akan mulki.

Sakon Dan Buran na Kauru ya nuna irin godiya da yadda tsarin shugabancin mai martaba da irin gudummuwar da ya ke bayarwa ga bunkasar al’ummar yankin a wadannan shekarun 3.

Yusuf Zubairu

Labarai

Labarai7 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara