Connect with us

Labarai

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Published

on

Daga Aminu Dalhatu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na farko na Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa da ke Gusau.

Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Abubakar Mohammad Nakwada ne ya bayyana hakan a Gusau, inda ya ce naɗin wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatin wajen tabbatar da ingantaccen tsari da kuma shirya filin jirgin domin fara aiki nan ba da jimawa ba.

A cikin wata sanarwa da Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai ga Sakataren Gwamnatin Jihar, Sulaiman Ahmad Tudu ya fitar,  ana sa ran filin jirgin zai ƙara bunƙasa haɗin kai na zirga-zirgar jiragen sama zuwa ƙasashen waje, da jawo damar zuba jari, tare da ƙarfafa ci gaban tattalin arziƙi a Jihar Zamfara da ma Najeriya baki ɗaya.

Sanarwar ta ce Kabir Yahaya Gusau ƙwararren masani ne a fannin harkokin sufurin jiragen sama, wanda ya shafe sama da shekaru talatin yana aiki a fannoni daban-daban na gudanar da ayyukan jiragen sama da sarrafa sararin samaniya.

Ya riƙe muƙamai masu muhimmanci a fannin sufurin jiragen sama a Najeriya, ciki har da Manajan Sararin Samaniya a Hukumar Kula da Sararin Samaniya ta Kasa a Filin Jirgin Sama na Gombe, da kuma Mataimaki na Musamman ga Manajan Darakta kuma Babban Jami’in Hukumar.

Kafin wannan naɗi, shi ne Babban Manaja na Sashen Bayanan Sufurin Jiragen Sama (Aeronautical Information Services) a hedikwatar Hukumar Kula da Sararin Samaniya ta Kasa da ke Abuja.

Gwamna Dauda Lawal ya buƙaci sabon Daraktan Janar ɗin da ya yi amfani da gogewarsa wajen tabbatar da ingantaccen tsari da gudanar da ayyukan filin jirgin yadda ya kamata, bisa ƙa’idojin sufurin jiragen sama na duniya.

Labarai

Labarai18 hours ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai19 hours ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai20 hours ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai2 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai3 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi3 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai3 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai3 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Mafi Shahara