Connect with us

Labaran Ketare

An kusa kulla yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza – Biden

Published

on

Shugaba Biden ya ce akwai fatan cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza nan da Litinin mai zuwa.

Kalaman shugaban Amurkan na zuwa ne yayin da rahotanni ke nuna alamun samun nasara a tattaunawar da ake yi tsakanin Isr’ila da Hamas ƙarƙashin jagorancin Qatar.

Da yake jawabi ga manema labarai a birnin New York, Mr Biden ya ce mai bashi shawara a kan tsaron ƙasa ya shaida masa cewa an kusa ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta, da kuma sakin mutanen da Hamas ta yi garkuwa da su.

Shugaba Biden ya ce bisa yadda abubuwa ke tafiya, nan da ranar Litinin za a sanar da batun tsagaita wutar.

Isra’ila da Hamas na ci gaba da tattauna yadda shirin tsagaita wutar zai kasance, a wani zama da wakilan ɓangarorin ke yi a Qatar.

Akwai rahotannin cewa za a sako fursunonin Falasɗinawa har 400 da ke tsare a Isra’ila, domin neman Hamas ta sako wa Isra’ilan mata 40, mafi yawan su dattijai ne.

Firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu dai ya sha alwashin ci gaba da shirinsa na luguden wuta a birnin Rafah da ke kudancin Gaza, ko da kuwa an cimma yarjejeniyar tsagaita wutar.

Can kuwa a gaɓar yamma da kogin Jordan, rahotanni sun ce an kashe Falasɗinawa uku a wata aran-gama da dakarun Isra’ila.

Hukumar lafiyar Falasɗinawan ta ce mutum aƙalla dubu huɗu aka kashe a gaɓar yamma da kogin Jordan tun da aka fara yaƙin a Gaza.

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara