Fasaha
Kotu ta tursasa a sauya sunan zakunan da aka yi wa laƙabi da abin bautar Hindu
Kotu a ke Indiya ta umarci wani gidan yari da ke jihar West Bengal ya canza wa wasu zakuna suna bayan wata ƙungiyar mabiya addinin Hindu ta yi koken cewa hakan saɓo ne ga addininsu.
Zakanya ta farko, tun asali an laƙaba mata suna wanda ya samo asali daga abar bautar mabiya addinin Hindu da ake kira Sita, sai kuma zakin da ake kira Akbar wanda shi ma ya samo asali daga wani jagora na daular Mughal a ƙarni na 16.
Ƙungiyar mabiya Hindu ta Vishwa Hindu Parishad ce ta ƙalubalanci hakan a kotu, kan cewa sunan da aka bai wa zakanyar saɓo ne a addinin Hindu.
A ranar Alhamis, kotun ta ce a daina sanya wa dabbobi sunayen abin bautar Hindu ko na annabawan Musulunci ko manyan malaman Kiristoci da na mutanen da suka lashe kyautukan Nobel da kuma na ƴan rajin ƙwatar ƴanci.
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United