Hukumar a shafinta na X ta wallafa hotunan kayayyakin da ta ƙwace daga hannun mutanen da ake zargi da tafka almundahanar da intanet.
A cewar EFCC, ba da daɗewa bane za a gurfanar da mutanen a gaban kotu da zarar an kammala bincike.
Hukumomi a Najeriya sun kama mutum 50 da ake zargi da aikata almundahana ta intanet, akasarinsu ɗaliban jami’ar jihar Kwara.
Hukumar EFCC mai yaƙi da yi wa arzikin ƙasa zagon ƙasa cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis ta ce an kama ɗalibai 48 da wasu mutum biyu a maɓoyansu daban-daban sakamakon kwanakin da aka shafe ana sa ido.
EFCC ta ce ta gano wasu motocin ƙasaita tara sai kwamfutocin laptop 24 da kuma wayoyin hannu daban-daban a hannun mutanen da ake zargi, waɗanda aka ce suna rayuwa ta facaka.
Hukumar ta kuma ce jami’anta sun bazama domin fitar da ƙasar daga ƙangin rashawa da sauran miyagun laifuka da ƴan yahoo ke yi.
Hukumar a shafinta na X ta wallafa hotunan kayayyakin da ta ƙwace daga hannun mutanen da ake zargi da tafka almundahanar da intanet.
A cewar EFCC, ba da daɗewa bane za a gurfanar da mutanen a gaban kotu da zarar an kammala bincike.
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
Varane zai bar Manchester United