Connect with us

Labarai

An Kashe Makiyaya 2 Da Shanu 150 A Sabon Hari A Filato

Published

on

Aƙalla makiyaya biyu da shanu 150 ne rahotanni suka ce wasu ‘yan bindiga sun kashe a wani hari da suka kai gundumar Kwal da ke Ƙaramar hukumar Bassa a Jihar Filato.

A cewar shugabannin Fulani a jihar, an kuma yi awon gaba da shanu sama da 100 a lokacin da lamarin ya faru.

Shuwagabannin Ƙungiyar Miyetti Allah (MACBAN) da na takwararta Gan Allah Fulani (GAFDAN), Nura Abdullahi da Garba Abdullahi, sun tabbatar da faruwar lamarin a ranar Juma’a.

Sun bayyana cewa akwai yiwuwar adadin shanun da aka kashe sun kai fiye da 150, yayin da wasu da dama suka ɓace.

Da yake bayyana lamarin, shugaban GAFDAN ya ce, “Makiyayan suna kiwon shanunsu ne da misalin ƙarfe 9:00 na safiyar Laraba, kwatsam wasu ‘yan bindiga suka buɗe musu wuta.

“Sun harbe makiyaya biyu har lahira. Har ila yau, sun harbe ɗaruruwan shanu, inda suka kashe kimanin 150.

“Har yanzu ba mu tabbatar da yawan ɓarnar ba, domin lamarin ya faru ne a wani wuri mai nisa da ke da wahalar shiga, ba tare da jami’an tsaro ba. Mun yi babban rashi.

“Lokaci ya yi da jami’an tsaro za su ɗauki mataki kan ta’asar da ake yi wa mutanenmu.

“A duk lokacin da aka kai mana hari, sai jami’an tsaro su nemi mu kwantar da hankalinmu.

“Wannan yunƙuri ne na halaka mu, kasancewar hari ne na ba gaira ba dalili. Muna kira ga hukumomin tsaro da su kawo mana agaji.”

Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar wanzar da zaman lafiya ta ‘Operation Safe Haven’ a jihar, Manjo Samson Zhakom, sai dai haƙar ba ta cimma ruwa ba har ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

Labarai

Labarai12 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi12 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai13 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai15 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai1 day ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara