Labarai
An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau
Daga Aminu Dalhatu
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na farko na Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa da ke Gusau.
Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Abubakar Mohammad Nakwada ne ya bayyana hakan a Gusau, inda ya ce naɗin wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatin wajen tabbatar da ingantaccen tsari da kuma shirya filin jirgin domin fara aiki nan ba da jimawa ba.
A cikin wata sanarwa da Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai ga Sakataren Gwamnatin Jihar, Sulaiman Ahmad Tudu ya fitar, ana sa ran filin jirgin zai ƙara bunƙasa haɗin kai na zirga-zirgar jiragen sama zuwa ƙasashen waje, da jawo damar zuba jari, tare da ƙarfafa ci gaban tattalin arziƙi a Jihar Zamfara da ma Najeriya baki ɗaya.
Sanarwar ta ce Kabir Yahaya Gusau ƙwararren masani ne a fannin harkokin sufurin jiragen sama, wanda ya shafe sama da shekaru talatin yana aiki a fannoni daban-daban na gudanar da ayyukan jiragen sama da sarrafa sararin samaniya.
Ya riƙe muƙamai masu muhimmanci a fannin sufurin jiragen sama a Najeriya, ciki har da Manajan Sararin Samaniya a Hukumar Kula da Sararin Samaniya ta Kasa a Filin Jirgin Sama na Gombe, da kuma Mataimaki na Musamman ga Manajan Darakta kuma Babban Jami’in Hukumar.
Kafin wannan naɗi, shi ne Babban Manaja na Sashen Bayanan Sufurin Jiragen Sama (Aeronautical Information Services) a hedikwatar Hukumar Kula da Sararin Samaniya ta Kasa da ke Abuja.
Gwamna Dauda Lawal ya buƙaci sabon Daraktan Janar ɗin da ya yi amfani da gogewarsa wajen tabbatar da ingantaccen tsari da gudanar da ayyukan filin jirgin yadda ya kamata, bisa ƙa’idojin sufurin jiragen sama na duniya.
-
Labarai6 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai6 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai6 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai3 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai7 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai6 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai3 days agoGwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya
-
Labarai5 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
