Connect with us

Labarai

BUK Ta Haramta “Signing-Out” A Harabar Jami’ar

Published

on

Mahukuntan jami’ar Bayero Kano sun sanar da haramta duk wasu bukukuwan “signing-out” da kuma amfani da rigunan kammala karatu ba tare da izini ba a harabar jami’ar.

A cikin wata sanarwa da Daraktan Harkokin Jama’a, Lamara Garba, ya sanya wa hannu a madadin Magatakardan jami’ar ta bayyana damuwarta kan yadda ake samun karuwar bukukuwan “signing-out” da daliban da ke shirin kammala karatu ke yi.

Sanarwar ta ce daga yanzu an haramta duk wani nau’i na wadannan bukukuwa. Hakan ya hada da sanya tufafin da aka lalata ko aka rubuta a jikinsu, amfani da fenti, tawada ko alamar rubutu a jiki ko a kadarorin jami’a, tayar da tarzoma ko hayaniya a bainar jama’a, da duk wasu ayyuka makamantan haka da ake yi da sunan murnar kammala karatu.

Haka kuma, mahukuntan jami’ar sun hana daliban da ke shirin kammala karatu amfani da rigunan kammala karatu (academic gowns) ko wasu tufafi na musamman domin daukar hotuna ko gudanar da bukukuwa ba bisa ka’ida ba a cikin harabar jami’a. Sun jaddada cewa rigunan kammala karatu an tanade su ne kawai domin bukukuwan da jami’a ta amince da su a hukumance.

Sanarwar ta yi gargadin cewa duk wani dalibi ko gungun dalibai da aka samu suna aikata irin wadannan abubuwa za a hukunta su bisa tanadin dokoki da ka’idojin jami’ar.

Jami’ar ta kuma tunatar da dalibai cewa bayar da shaidar digiri ba ya ta’allaka ga nasarar karatu kadai ba, har ma da kyawawan halaye da da’a. Don haka, an bukaci daliban da ke kammala karatu su nuna hali da ɗabi’ar da za su kare mutunci da martabar jami’ar.

Haka zalika, an umarci jami’an tsaro su tabbatar da cikakken bin wannan umarni tare da kama duk wanda ya karya dokar.

Jami’ar ta shawarci dukkan dalibai da su yi biyayya da wannan umarni yadda ya kamata.

Khadijah Aliyu/Kano

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara