Kasuwanci
Gwamna AbdulRazaq Ya Yi Jimamin Kisan Jami’in Gandun Daji
Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa kan rasuwar wani jami’in gandun daji, Omotosho Olawuyi Samuel, wanda ya rasa ransa yayin artabu da wasu ’yan bindiga masu garkuwa da mutane a ƙauyen Koro, da ke Ƙaramar Hukumar Ekiti ta jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Rafiu Ajakaye, ya fitar, gwamnan ya yaba da jarumtaka da kishin ƙasa da jami’an gandun daji da ’yan sa-kai na tsaro na al’umma suka nuna, inda suka kai farmaki kan ’yan bindigar da ke tserewa.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa gwamnatin jihar za ta bayar da tallafin naira miliyan goma (₦10m) ga iyalan mamacin jami’in, a matsayin alamar godiya da jin daɗin gwamnati bisa sadaukarwar rayuwarsa.
Haka zalika, sanarwar ta miƙa ta’aziyya ga iyalan Omotosho Olawuyi Samuel da kuma abokan aikinsa da suka yi yaƙi tare da shi cikin jarumta.
ALI MUHAMMAD RABIU
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
