Labarai
Jam’iyyatut Takaful Aytam Ta Ziyarci Marasa Lafiya A Asibiti Dake Kaduna
Kungiyar Jam’iyyatut Takaful Aytam dake Kaduna ta ba da gudunmuwar kuɗi ga marasa lafiya dake kwance a asibitin Yusuf Dantsoho dake Kaduna.
Shugabar kungiyar, Malama Rabi’atu Adam Isma’il wadda ta jagoranci wakilan kungiyar zuwa asibitin, tace, wannan wani bangare ne na ayyukanta, su taimakawa mabukata a lokacin wannan wata mai albarka na Ramadan.
Malama Rabi’atu Adam Isma’il ta yi bayanin cewa, yana daga cikin koyarwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad SAW a ziyarci mara lafiya da ciyarda marayu da marasa karfi a lokacin azumin watan Ramadan da sauran lokuta.
Ta yi nuni da cewa, ba gwamnati ko wasu kungiyoyin kasashen waje ke tallafawa kungiyar ba, suna samun kudadensu ne ta hanyar tara taro-sisi a tsakanin wakilan kungiyar da wasu daidaikun jama’a.
Malama Rabi’atu Adam Isma’il ta ce, kungiyar, ta baiwa kusan kowane majinyaci naira dubu wanda babu yawa, sai dai zai taimaka ma marasa lafiyan wajen sayen magani ko kayan marmari.
Ta nemi ganin gwamnati da mawadata da kungiyoyi masu zaman kansu su tallafawa kungiyar domin ta yi abinda ya fi haka a gaba wajen yi wa al’uma hidima.
A nata tsokacin, mataimakiyar shugabar kungiyar, Malama Ruqayya Ahmad Bashir ta ce, wakilai da abokanan kungiyar ne suka yanke shawarar harhada dan abinda Allah Ya hore musu domin tallafawa marasa lafiyan dake kwance a asibiti.
Ta kara da cewa, sun baiwa marasa lafiyan gudunmuwar ne ta hanyar nuna soyayya da tausayi, ta yi musu addu’ar samun lafiya cikin gaggawa.
Wasu daga cikin wadanda suka amfana, Saleh Muhammad da Fatima Umar sun yabawa jagororin kungiyar akan tallafin kudin, sun yi addu’ar Allah Ya sa ka musu da mafificin sakamako.
Kungiyar ta ziyarci babban dakin marasa lafiya da dakin masu karaya ko quna da kuma dakin masu hatsari.
Khadija Kubau
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United