Connect with us

Labarai

Jam’iyyatut Takaful Aytam Ta Ziyarci Marasa Lafiya A Asibiti Dake Kaduna 

Published

on

Kungiyar Jam’iyyatut Takaful Aytam dake Kaduna ta ba da gudunmuwar kuɗi ga marasa lafiya dake kwance a asibitin Yusuf Dantsoho dake Kaduna.

 

Shugabar kungiyar, Malama Rabi’atu Adam Isma’il wadda ta jagoranci wakilan kungiyar zuwa asibitin, tace, wannan wani bangare ne na ayyukanta, su taimakawa mabukata a lokacin wannan wata mai albarka na Ramadan.

Malama Rabi’atu Adam Isma’il ta yi bayanin cewa, yana daga cikin koyarwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad SAW a ziyarci mara lafiya da ciyarda marayu da marasa karfi a lokacin azumin watan Ramadan da sauran lokuta.

 

Ta yi nuni da cewa, ba gwamnati ko wasu kungiyoyin kasashen waje ke tallafawa kungiyar ba, suna samun kudadensu ne ta hanyar tara taro-sisi a tsakanin wakilan kungiyar da wasu daidaikun jama’a.

 

Malama Rabi’atu Adam Isma’il ta ce, kungiyar, ta baiwa kusan kowane majinyaci naira dubu wanda babu yawa, sai dai zai taimaka ma marasa lafiyan wajen sayen magani ko kayan marmari.

 

Ta nemi ganin gwamnati da mawadata da kungiyoyi masu zaman kansu su tallafawa kungiyar domin ta yi abinda ya fi haka a gaba wajen yi wa al’uma hidima.

 

A nata tsokacin, mataimakiyar shugabar kungiyar, Malama Ruqayya Ahmad Bashir ta ce, wakilai da abokanan kungiyar ne suka yanke shawarar harhada dan abinda Allah Ya hore musu domin tallafawa marasa lafiyan dake kwance a asibiti.

 

Ta kara da cewa, sun baiwa marasa­ lafiyan gudunmuwar ne ta hanyar nuna soyayya da tausayi, ta yi musu addu’ar samun lafiya cikin gaggawa.

Wasu daga cikin wadanda suka amfana, Saleh Muhammad da Fatima Umar sun yabawa jagororin kungiyar akan tallafin kudin, sun yi addu’ar Allah Ya sa ka musu da mafificin sakamako.

 

Kungiyar ta ziyarci babban dakin marasa lafiya da dakin masu karaya ko quna da kuma dakin masu hatsari.

 

Khadija Kubau

Labarai

Labarai22 mins ago

Kungiyar CAN Ta Rasa Mata Shida A Hadarin Mota A Taraba

An bayyana cewa wasu ’yan kungiyar mata ta kungiyar Kiristoci ta Najeriya (WOWICAN) su shida ne suka rasa rayukansu a...

Labarai36 mins ago

‘Yan Sakai Jihar Taraba Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Yi Garkuwa

Rundunar ‘yan banga ta Najeriya (VGN) reshen jihar Taraba ta yi nasarar ceto wasu mutane uku da aka yi garkuwa...

Ilimi48 mins ago

Talatar Nan Jirgin farko na Maniyatan jihar Kwara Zai Tashi

An dage tashin jirgin farko daga filin jirgin sama na Janar Tunde Idiagbon na kasa da kasa na Ilorin don...

Labarai1 hour ago

HARIN MASALLACIN KANO: Obi Ya Ziyarci Wadanda suka Mutu

  Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LP) a zaben 2023, Peter Obi, ya ziyarci wadanda kona masallacin Kano...

Labarai1 hour ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi Ta Yi Kiran A Yiwa Mijinta Addu’a

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta ce addu’a ita ce ginshikin duk wani shugabanci mai nasara, don...

Labarai2 hours ago

Gwamnatin Kano Ta Rufe Asibitin Kwanar Ganduje A Kano

Gwamnatin jihar Kano, ta rufe tare asibitin Kwanar Ganduje dake unguwar Sharada Karamar Hukumar Kano Municipal.   Babban daraktan hukumar...

Labarai2 hours ago

Shugaban Iran Ebrahim Raisi Ya Rasu A Hatsarin Jirgi

Jami’an Iran sun ce Shugaba Ebrahim Raisi da ministan harkokin wajen ƙasar, Hossein Amir-Abdollahian sun rasu a wani hatsarin jirgin...

Labarai13 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Mafi Shahara