Kasuwanci
Gwamnatin Sakkwato Ta Kashe Naira Miliyan 60 Kan Koyon Sana’o’i
Gwamnatin Jihar Sakkwato ta kaddamar da rabon kuɗaɗe har Naira miliyan sittin ga matasa dari shida da aka horas a sana’o’i daban-daban a ƙarƙashin shirin koyon sana’o’i na jihar.
A yayin bikin miƙa takardun cekin kudin ga waɗanda suka ci gajiyar shirin, gwamnan jihar, wanda Mai Ba Shi Shawara na Musamman kan Cigaban Al’umma, Alhaji Garba Maitumbi Kebbe ya wakilta, ya bayyana cewa shirin horaswar an tsara shi ne domin ƙarfafa matasa su dogara da kansu tare da ba da gudummawa wajen bunƙasa ci gaban jihar.
Ahmad Aliyu ya ce gwamnatinsa na da cikakken ƙuduri na tallafa wa bunƙasar ƙananan da matsakaitan masana’antu, a matsayin muhimmin ginshiƙi na bunƙasar tattalin arzikin jihar.
A nata jawabin, Babbar Sakatariyar Hukumar Bunƙasa Ƙananan da Matsakaitan Masana’antu ta Jihar Sakkwato (SOSMEDA), Hajiya Binta Usman, ta ce waɗanda suka amfana da shirin—waɗanda SOSMEDA tare da Sashen Cigaban Al’umma suka horas—sun karɓi Naira dubu ɗari-ɗari kowannensu tare da kayan aikin sana’a domin tallafa musu wajen fara kasuwanci.
Ta ƙara da cewa hukumar ta riga ta horas da matasa sama da dubu uku da ɗari bakwai da hamsin a faɗin jihar.
NASIR MALALI
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
