Connect with us

Kasuwanci

Gwamnatin Sakkwato Ta Kashe Naira Miliyan 60 Kan Koyon Sana’o’i

Published

on

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta kaddamar da rabon kuɗaɗe har Naira miliyan sittin ga matasa dari shida da aka horas a sana’o’i daban-daban a ƙarƙashin shirin koyon sana’o’i na jihar.

A yayin bikin miƙa takardun cekin kudin ga waɗanda suka ci gajiyar shirin, gwamnan jihar, wanda Mai Ba Shi Shawara na Musamman kan Cigaban Al’umma, Alhaji Garba Maitumbi Kebbe ya wakilta, ya bayyana cewa shirin horaswar an tsara shi ne domin ƙarfafa matasa su dogara da kansu tare da ba da gudummawa wajen bunƙasa ci gaban jihar.

Ahmad Aliyu ya ce gwamnatinsa na da cikakken ƙuduri na tallafa wa bunƙasar ƙananan da matsakaitan masana’antu, a matsayin muhimmin ginshiƙi na bunƙasar tattalin arzikin jihar.

A nata jawabin, Babbar Sakatariyar Hukumar Bunƙasa Ƙananan da Matsakaitan Masana’antu ta Jihar Sakkwato (SOSMEDA), Hajiya Binta Usman, ta ce waɗanda suka amfana da shirin—waɗanda SOSMEDA tare da Sashen Cigaban Al’umma suka horas—sun karɓi Naira dubu ɗari-ɗari kowannensu tare da kayan aikin sana’a domin tallafa musu wajen fara kasuwanci.

Ta ƙara da cewa hukumar ta riga ta horas da matasa sama da dubu uku da ɗari bakwai da hamsin a faɗin jihar.

NASIR MALALI

Labarai

Labarai18 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi18 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai18 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai20 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara