Labarai
NLC Ta Gudanar da Gangamin Lumana a Kano
Daga Abdullahi Jalaluddeen
Kungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC) ta gudanar da gangamin lumana a jihar Kano domin jawo hankalin jama’a kan ƙalubalen tsaro da ke addabar ƙasa, tare da miƙa wasikar bukatu ga Gwamnatin Jihar Kano.
Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnatin Jihar Kano, Dakta Suleiman Sani Wali, wanda ya wakilci Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya ce gwamnatin jihar na da kyakkyawar alaka da ƙungiyoyin ƙwadago, inda ya bayyana gangamin a matsayin shaida ta zaman lafiya da fahimta tsakanin gwamnati da ma’aikata.
Ya bayyana gamsuwarsa bisa yadda aka gudanar da gangamin cikin lumana da tsari, yana mai cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da jajircewa wajen yin mu’amala mai kyau da ƙungiyoyin ƙwadago.
Shugaban Ma’aikatan ya tabbatar wa NLC cewa ana ɗaukar batutuwan tsaro da muhimmanci a jihar, inda ya ce dukkan hukumomin tsaro na aiki gwargwadon ƙarfinsu domin ci gaba da tabbatar da zaman lafiya a Kano.
Ya kuma ce gwamnan zai duba wasikar da NLC ta gabatar tare da tabbatar da cewa an isar da abubuwan da ke cikinta ga hukumomin da suka dace, ciki har da Shugaban Ƙasa.
Tun da fari, wakilin Shugaban NLC na ƙasa, Mista Muttaqa Yusha’u, ya ce gangamin ya yi daidai da kudurin Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na NLC na shirya gangamin lumana a fadin ƙasar domin wayar da kan jama’a kan matsalar rashin tsaro da kuma inganta zaman lafiya.
Yusha’u ya jaddada cewa rashin tsaro na shafar ma’aikata a kowane fanni, ciki har da malamai, ma’aikatan lafiya, manoma, ’yan kasuwa da jami’an tsaro, yana mai cewa ba za a samu ci gaba ba tare da tsaro da zaman lafiya ba.
Ya yi kira da a samar da tsarin hadin gwiwa tsakanin gwamnatocin tarayya, jihohi da kananan hukumomi, tare da shugabannin al’umma da ƙungiyoyin ma’aikata, domin shawo kan matsalolin tsaro yadda ya kamata.
Haka nan, Shugaban NLC na Jihar Kano, Mista Kabiru Inuwa, ya yaba wa Gwamnatin Jihar Kano bisa ci gaba da tabbatar da zaman lafiya a jiharjisai dai ya bukaci a ƙara ƙaimi domin hana yaɗuwar rashin tsaro daga sauran sassan ƙasar.
Inuwa ya jaddada buƙatar inganta walwala da tallafi ga jami’an tsaro da iyalansu, yana mai bayyana cewa haɗin gwiwa tsakanin gwamnatoci da ƙungiyoyin ƙwadago shi ne hanya mafi dacewa ta samar da tsaro mai ɗorewa.
Kungiyar NLC ta sake jaddada aniyar ta na goyon bayan duk wata gwamnati da ke bada fifiko ga walwalar ma’aikata, zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki da zamantakewa.
-
Labarai7 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai7 days agoGwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya
-
Labarai7 days agoSojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina
-
Labarai4 days agoAn Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau
-
Labarai7 days agoNSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara
-
Labarai7 days agoNCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji
-
Labarai4 days agoKwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara
-
Labarai4 days agoTinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa
