Connect with us

Labarai

NLC Ta Gudanar da Gangamin Lumana a Kano

Published

on

Daga Abdullahi Jalaluddeen

Kungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC) ta gudanar da gangamin lumana a jihar Kano domin jawo hankalin jama’a kan ƙalubalen tsaro da ke addabar ƙasa, tare da miƙa wasikar bukatu ga Gwamnatin Jihar Kano.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnatin Jihar Kano, Dakta Suleiman Sani Wali, wanda ya wakilci Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya ce gwamnatin jihar na da kyakkyawar alaka da ƙungiyoyin ƙwadago, inda ya bayyana gangamin a matsayin shaida ta zaman lafiya da fahimta tsakanin gwamnati da ma’aikata.

Ya bayyana gamsuwarsa bisa yadda aka gudanar da gangamin cikin lumana da tsari, yana mai cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da jajircewa wajen yin mu’amala mai kyau da ƙungiyoyin ƙwadago.

Shugaban Ma’aikatan ya tabbatar wa NLC cewa ana ɗaukar batutuwan tsaro da muhimmanci a jihar, inda ya ce dukkan hukumomin tsaro na aiki gwargwadon ƙarfinsu domin ci gaba da tabbatar da zaman lafiya a Kano.

Ya kuma ce gwamnan zai duba wasikar da NLC ta gabatar tare da tabbatar da cewa an isar da abubuwan da ke cikinta ga hukumomin da suka dace, ciki har da Shugaban Ƙasa.

Tun da fari, wakilin Shugaban NLC na ƙasa, Mista Muttaqa Yusha’u, ya ce gangamin ya yi daidai da kudurin Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na NLC na shirya gangamin lumana a fadin ƙasar domin wayar da kan jama’a kan matsalar rashin tsaro da kuma inganta zaman lafiya.

Yusha’u ya jaddada cewa rashin tsaro na shafar ma’aikata a kowane fanni, ciki har da malamai, ma’aikatan lafiya, manoma, ’yan kasuwa da jami’an tsaro, yana mai cewa ba za a samu ci gaba ba tare da tsaro da zaman lafiya ba.

Ya yi kira da a samar da tsarin hadin gwiwa tsakanin gwamnatocin tarayya, jihohi da kananan hukumomi, tare da shugabannin al’umma da ƙungiyoyin ma’aikata, domin shawo kan matsalolin tsaro yadda ya kamata.

Haka nan, Shugaban NLC na Jihar Kano, Mista Kabiru Inuwa, ya yaba wa Gwamnatin Jihar Kano bisa ci gaba da tabbatar da zaman lafiya a jiharjisai dai ya bukaci a ƙara ƙaimi domin hana yaɗuwar rashin tsaro daga sauran sassan ƙasar.

Inuwa ya jaddada buƙatar inganta walwala da tallafi ga jami’an tsaro da iyalansu, yana mai bayyana cewa haɗin gwiwa tsakanin gwamnatoci da ƙungiyoyin ƙwadago shi ne hanya mafi dacewa ta samar da tsaro mai ɗorewa.

Kungiyar NLC ta sake jaddada aniyar ta na goyon bayan duk wata gwamnati da ke bada fifiko ga walwalar ma’aikata, zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki da zamantakewa.

Labarai

Labarai3 days ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai3 days ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Labarai3 days ago

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Yi Rijista a Jam’iyyar APC

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Malam Mummuni, ya yi rijista a hukumance a matsayin cikakken ɗan jam’iyyar APC. An...

Labarai3 days ago

Jami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta yi martani kan zarge-zargen da ke yawo cewa wani mutum da ake zargin yana ikirarin...

Labarai3 days ago

Matashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba

Wani matashi mai digirin na 2 a fannin Ilimin (Theology) kuma wanda ya kammala karatun Physics, mai suna Hilekann Eric,...

Labarai4 days ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai4 days ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai4 days ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai5 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai6 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Mafi Shahara