Connect with us

Ilimi

Gwamna Lawal Ya Nada Sabon Shugaban Jami’ar Jihar Zamfara

Published

on

Daga Aminu Dalhatu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Farfesa Ibrahim Abdullahi Tsafe a matsayin sabon Shugaban Jami’ar Jihar Zamfara da ke Talata Mafara (ZAMSUT), na wa’adin shekara biyar kacal.

Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Abubakar Mohammad Nakwada ne ya sanar da wannan naɗin ta hannun Babban Mataimakinsa na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Sulaiman Ahmad Tudu.

Ya bayyana cewa naɗin ya biyo bayan shawarwarin Majalisar Gudanarwar Jami’ar.

Farfesa Tsafe fitaccen malami ne wanda ya samu digirin Digirgir (PhD) a shekarar 2006, kuma Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sokoto (UDUS) ta ɗaga shi zuwa matsayin Farfesa a shekarar 2013.

Ya rike mukamai daban-daban na gudanarwa, ciki har da zama shugaban Tsangayar Nazarin Halittu da Sinadarai  a UDUS. Haka kuma, ya yi aiki a matsayin Visiting Professor a ZAMSUT tun shekarar 2018, kuma a halin yanzu shi ne shugaban tsangayar kimiyya a jami’ar.

Gwamna Lawal ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa Farfesa Tsafe zai yi amfani da ƙwarewarsa da gogewarsa wajen ɗaga darajar Jami’ar ZAMSUT zuwa matsayi mafi girma, bisa manufar gwamnatinsa ta bunƙasa ilimi da nagartar karatu.

Labarai

Labarai17 hours ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai18 hours ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai19 hours ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai2 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai3 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi3 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai3 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai3 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Mafi Shahara