Ilimi
Gwamna Lawal Ya Nada Sabon Shugaban Jami’ar Jihar Zamfara
Daga Aminu Dalhatu
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Farfesa Ibrahim Abdullahi Tsafe a matsayin sabon Shugaban Jami’ar Jihar Zamfara da ke Talata Mafara (ZAMSUT), na wa’adin shekara biyar kacal.
Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Abubakar Mohammad Nakwada ne ya sanar da wannan naɗin ta hannun Babban Mataimakinsa na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Sulaiman Ahmad Tudu.
Ya bayyana cewa naɗin ya biyo bayan shawarwarin Majalisar Gudanarwar Jami’ar.
Farfesa Tsafe fitaccen malami ne wanda ya samu digirin Digirgir (PhD) a shekarar 2006, kuma Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sokoto (UDUS) ta ɗaga shi zuwa matsayin Farfesa a shekarar 2013.
Ya rike mukamai daban-daban na gudanarwa, ciki har da zama shugaban Tsangayar Nazarin Halittu da Sinadarai a UDUS. Haka kuma, ya yi aiki a matsayin Visiting Professor a ZAMSUT tun shekarar 2018, kuma a halin yanzu shi ne shugaban tsangayar kimiyya a jami’ar.
Gwamna Lawal ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa Farfesa Tsafe zai yi amfani da ƙwarewarsa da gogewarsa wajen ɗaga darajar Jami’ar ZAMSUT zuwa matsayi mafi girma, bisa manufar gwamnatinsa ta bunƙasa ilimi da nagartar karatu.
-
Labarai7 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai6 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai6 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai3 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai6 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai7 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai5 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
