Labarai
Fadar Shugaban Kasar Benin ta ce Har Yanzu Talon Ne a Kan Mulki
Gwamnatin Jamhuriyar Benin ta bayyana cewa ta dakile wani yunkurin juyin mulki, bayan da wasu sojojin ƙasar suka sanar da cewa sun hambarar da shugaba Patrice Talon a gidan talabijin na kasar.
Talon, mai shekaru 67, tsohon dan kasuwa ne wanda aka yiwa lakabi da “Sarkin Auduga na Cotonou”, zai mika mulki a watan Afrilun shekara ta 2025 dake ƙaratowa, bayan shafe shekaru 10 a kan karagar mulki wanda ke nuna samun ci gaban tattalin arziki mai inganci.
Da sanyin safiyar Lahadi ne sojojin da ke kiran kansu da suna “Kwamitin Soji na sake farfado da ƙasa” (CMR), suka gabatar da wata sanarwa a gidan talabijin na kasar cewa sun gana kuma sun yanke shawarar cewa “An tsige shugaba Patrice Talon daga mukamin shugaban jamhuriyar”.
Sai dai jim kadan bayan sanarwar, wata majiya da ke kusa da Talon ta shaida wa kamfanin dillacin labaru na AFP cewa shugaban yana cikin koshin lafiya tare da yin Allah wadai da masu yunkurin juyin mulkin.
-
Labarai6 days agoAna Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka
-
Labarai6 days agoJam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano
-
Labarai5 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoGwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya
-
Labarai4 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai4 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara
