Connect with us

Labarai

Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Majalisar Abinci Mai Gina Jiki ta Jihar Jigawa

Published

on

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya kaddamar da Majalisar Abinci Mai Gina Jiki ta Jihar Jigawa 774, inda ya tabbatar da kudurin gwamnatinsa na yaki da rashin abinci mai gina jiki da inganta yalwar abinci a fadin jihar.

An gudanar da kaddamarwar ne yayin ziyarar Mrs. Uju Rochas-Anwuka, mai bai wa Shugaban Kasa shawara ta musamman kan lafiya ( Karkashin Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa), wacce ta je Jigawa domin kaddamar da shirin Nutrition 774 da ke karkashin shirin sabunta kudurori na Renewed Hope Agenda.

Gwamna Namadi ya bayyana cewa Jigawa ta kasance gaba a yaki da matsalar, tare da kafa shiri na musamman da aka yi wa lakabi da Masaki tun a 2020 domin fadakar da al’umma a matakin ƙasa, wanda ya amfanar da sama da mutum miliyan 1 da dubu 300.

Ya kara da cewa gwamnati na ware Naira Miliyan 13 da rabi a kowane wata domin tallafa wa shirin  na Masaki, da kuma Naira Miliyan 250 a shekara, don sayen abinci da magani tare da UNICEF, yayin da Majalisar Dokoki ke bayar da Naira Miliyan 300 a shekara.

Haka kuma, sama da mata 600 sun samu horo a shirin abincin yara na Tom Brown don samar da abinci mai gina jiki a gida tare da hadin gwiwar hukumar NAFDAC.

Gwamnan ya ce sabuwar majalisar za ta hada kai da ma’aikatun gwamnati wajen tsara da aiwatar da manufofin abinci mai gina jiki, tare da nufin sanya Jigawa ta zama ta farko da za ta cimma burin shirin gwamnatin tarayya naNutrition 774.

A jawabinta, Mrs Uju ta ce shirin na daga cikin manyan shirye-shiryen gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, da nufin magance matsalar rashin abinci mai gina jiki a fadin kasar.

 

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai10 hours ago

Tinubu Ya Nada Ibrahim Masari a Matsayin Mai Ba Shi Shawara Kan Harkokin Siyasa

Daga Bello Wakili Shugaban Ƙasa Bola Tinubu  ya naɗa Ibrahim Aminu Masari a matsayin Mai ba shi Shawara na Musamman...

Labarai11 hours ago

Kungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi

Daga Usman Muhammad Zaria  Wata ƙungiyar al’umma mai suna Hadejia Advocacy ta yaba wa Gwamnan  Jigawa, Umar Namadi, kan yadda...

Labarai17 hours ago

Ramadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu

Daga Yusuf Zubairu Kauru Sarkin Kauru da ke Jihar Kaduna, Alhaji Zakari Ya’u Shehu Usman, ya yi kira da a...

Labarai18 hours ago

Gwamnatin Jigawa Ta Sha Alwashin Bin Kadin Shari’ar Walida Abdulhadi

Daga Usman Muhammad Zaria  Gwamna Umar Namadi ya tabbatar da cewa Gwamnatin  Jigawa za ta bi sawun shari’ar sace ‘yar...

Labarai2 days ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi2 days ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai2 days ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai3 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai4 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Mafi Shahara