Labarai
Najeriya Na Kara Samun Tagomashi Karkashin Mulkin Tinubu- Fadar Shugaban Kasa
Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta samu ci gaba a fannoni daban-daban na tattalin arziƙi.
Sanarwar da mai ba Shugaban shawara kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga, ya fitar, ta ce ajiyar kuɗaɗen ƙasar na waje ya kai kusan Dala Biliyan 42 daga Dala Biliyan 32 da Tinubu ya tarar. Haka kuma gwamnati ta biya bashin sama da Dala Bliyan 7 ciki har da na kamfanonin jiragen sama.
Har ila yau, FFadar Shugaban Kasar ta musanta maganganun Atiku Abubakar na cewa yunwa da matsin tattalin arziƙi sun yi kamari, tana mai cewa kididdigar NBS ta nuna hauhawar farashi na raguwa tsawon watanni biyar, tare da samun ƙarin riba a harkokin kasuwanci.
Sanarwar ta ce gwamnati na ɗaukar matakan gyara kura-kuran baya, inda jihohi ke iya biyan albashi da fansho ba tare da jinkiri ba, kana kuma ana samun damar gudanar da ayyukan ci gaba.
Bayan shekaru biyu da watanni biyar kacal a ofis, gwamnatin yanzu ta bayyana alfahari da irin ci gaban da ake samu a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Daga Bello Wakili
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
