Labarai
BUK Ta Shirya Taro Kan Inganta Harkokin Kudi A Aikin Gwamnati
Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta sake jaddada kudirinta na ci gaba da samar da sauye-sauyen zamani wajen tafiyar da harkokin kuɗi a aikin gwamnati a Najeriya da sauran kasashen Afirka.
Shugaban jami’ar, Farfesa Haruna Musa ne ya bayyana wannan kudirin a taron ƙasa da ƙasa na farko kan harkokin mulkin jama’a, wanda sashen gudanarwa na jama’a, karkashin tsangayar nazarin harkokin tattalin arziki ta shirya.
Shugaban, wanda Mataimakiyar Shugaban Jami’a mai kula da Bincike da Cigaba, Farfesa Amina Mustapha ta wakilta, ya jaddada cewa BUK na kan gaba wajen jagorantar harkokin ilimi da suka dace da muradun ‘yan ƙasa bisa ƙa’idojin duniya.

Ya bayyana taken taron a matsayin abin da ya dace a wannan lokaci, tare da yin kira ga mahalarta da su yi amfani da ilimin da suka samu domin inganta tsarin mulki a Najeriya da Afirka.
A cikin saƙon fatan alheri, shugaban taron kuma Shugaban Hukumar Bincike da Cigaban Ilimin Najeriya (NERDC), Farfesa Salisu Shehu, ya jaddada canjin gaggawa da tattalin arzikin zamani ya haifar.
Ya ce Afirka na fuskantar sauye-sauye masu ban mamaki, kuma irin waɗannan taruka na zama tamkar ƙarfafa ingantaccen mulki da gaskiya ne a harkokin kudi.
Mai gabatar da muƙalar farko, Matawallen Zazzau kuma malami a Jami’ar Kaduna, wanda shi ne shugaban Hukumar Kula da Ma’aikatan Kananan Hukumomin Jihar Kaduna, Farfesa Aminu Ladan Sharehu, ya bayyana hanyoyin da Afirka musamman Najeriya za ta iya sauya manufofin jama’a da tsarin kuɗi domin haɓaka cigaba mai ɗorewa.

Ya lura cewa taron ya mai da hankali ne wajen nazarin yadda za a iya amfani da manufofin jama’a da tsarin kuɗi wajen inganta mulki mai nagarta.
Ɗaya daga cikin mahalarta taron, Mataimakin Daraktan Gudanarwa na Ƙaramar Hukumar Sabon Garin Jihar Kaduna, Nura Ibrahim Aminu, ya bayyana muhimmancin shirye-shiryen da al’umma suka jagoranta da kuma tarurrukan tattaunawa a yankuna wajen inganta gaskiya da cigaban ƙasa daga tushe.
Taron, na yini uku, mai taken “Sauya Manufofin Jama’a, Harkokin Kuɗi da Gudanarwa Domin Cigaba mai Ɗorewa a Afirka: Matsaloli, Kalubale da Hanyoyin Magance Su” ya samu mahalarta masana da dama daga ciki da wajen ƙasa.
Daga Khadijah Aliyu
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
