Connect with us

Labarai

BUK Ta Shirya Taro Kan Inganta Harkokin Kudi A Aikin Gwamnati

Published

on

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta sake jaddada kudirinta na ci gaba da samar da sauye-sauyen zamani wajen tafiyar da  harkokin kuɗi a aikin gwamnati a Najeriya da sauran kasashen Afirka.

Shugaban jami’ar, Farfesa Haruna Musa ne ya bayyana wannan kudirin a taron ƙasa da ƙasa na farko kan harkokin mulkin jama’a, wanda sashen gudanarwa na jama’a, karkashin tsangayar nazarin harkokin tattalin arziki ta shirya.

Shugaban, wanda Mataimakiyar Shugaban Jami’a mai kula da Bincike da Cigaba, Farfesa Amina Mustapha ta wakilta, ya jaddada cewa BUK na kan gaba wajen jagorantar harkokin ilimi da suka dace da muradun ‘yan ƙasa bisa ƙa’idojin duniya.

Ya bayyana taken taron a matsayin abin da ya dace a wannan lokaci, tare da yin kira ga mahalarta da su yi amfani da ilimin da suka samu domin inganta tsarin mulki a Najeriya da Afirka.

A cikin saƙon fatan alheri, shugaban taron kuma Shugaban Hukumar Bincike da Cigaban Ilimin Najeriya (NERDC), Farfesa Salisu Shehu, ya jaddada canjin gaggawa da tattalin arzikin zamani ya haifar.

Ya ce Afirka na fuskantar sauye-sauye masu ban mamaki, kuma irin waɗannan taruka na zama tamkar ƙarfafa ingantaccen mulki da gaskiya ne a harkokin kudi.

Mai gabatar da muƙalar farko, Matawallen Zazzau kuma malami a Jami’ar Kaduna, wanda shi ne shugaban Hukumar Kula da Ma’aikatan Kananan Hukumomin Jihar Kaduna, Farfesa Aminu Ladan Sharehu, ya bayyana hanyoyin da Afirka musamman Najeriya za ta iya sauya manufofin jama’a da tsarin kuɗi domin haɓaka cigaba mai ɗorewa.

Ya lura cewa taron ya mai da hankali ne wajen nazarin yadda za a iya amfani da manufofin jama’a da tsarin kuɗi wajen inganta mulki mai nagarta.

Ɗaya daga cikin mahalarta taron, Mataimakin Daraktan Gudanarwa na Ƙaramar Hukumar Sabon Garin Jihar Kaduna, Nura Ibrahim Aminu, ya bayyana muhimmancin shirye-shiryen da al’umma suka jagoranta da kuma tarurrukan tattaunawa a yankuna wajen inganta gaskiya da cigaban ƙasa daga tushe.

Taron, na yini uku, mai taken “Sauya Manufofin Jama’a, Harkokin Kuɗi da Gudanarwa Domin Cigaba mai Ɗorewa a Afirka: Matsaloli, Kalubale da Hanyoyin Magance Su” ya samu  mahalarta masana da dama daga ciki da wajen ƙasa.

 

Daga Khadijah Aliyu

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara