Labarai
Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Horas Da Yara Sana’o’i Tun Daga Matakin Firamare
Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada aniyarta na magance matsalar rashin aikin yi a tsakanin matasa ta hanyar samar da tsari na ƙasa kan haɓaka sana’o’in hannu daban daban.
An bayyana hakan ne a taron Cibiyar Horas da Sana’o’i ta Kasa da aka gudanar a Abuja ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, tare da Ministan Ilimi a matsayin mataimakinsa.
Bayan kammala taron, Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya bayyana cewa tattaunawar ta haifar da Ɗa mai ido, inda ya ce za a aika da kudirin kafa Cibiyar Horas da Sana’o’i ta Ƙasa zuwa majalisar dokoki nan ba da daɗewa ba.
Ya ce: “Manufar ita ce a daidaita ayyukan dukkan manyan masu ruwa da tsaki a wannan fanni. Kaduna ta riga ta amfana ƙwarai, inda Shugaba Bola Tinubu ya kaddamar da cibiyoyin koyon sana’o’i, inda dalibai sama 32,000 ke koyon sana’o’i daban daban.
Ministan Ilimi, Farfesa Tunji Alausa, ya jaddada cewa horar da sana’o’in hannu na kan gaba a cikin ajandar gwamnati, wacce ke daidai da alƙawarin Shugaba Tinubu na samar da damar ci gaba ga matasan Najeriya.
Ya bayyana cewa sabuwar manhajar ƙasa yanzu ta mai da hankali ne sosai kan fannoni na musamman guda shida, da suka hada da ɗinki, kiwon dabbobi, gyaran kwamfuta da wayoyin hannu, da sauransu, waɗanda su ne sana’o’in da kasa ke matukar bukata a yanzu.
Ita kuwa Minista a Ma’aikar Kwadago da Samar da Ayyuka, Nkeiruka Onyejeocha, ta bayyana cewa Majalisar Zartaswa na kokarin tabbatar da cewa yara na samun horo kan sana’o’in hannu tun daga matakin farko na ilimi har zuwa girmansu.
Ta ce “Manufar ita ce a tabbatar kowanne yaro ya girma da wata kwarewa, don rage tarin matasan da ba su da aiki. Haku kuma kowa zai samu damar taka muhimmiyar rawa a cikin al’umma.”
Bello Wakili
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
