Labarai
Builder Uba Ya Taya Sabon Shugaban ALGON Na Jihar Jigawa Murna
Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu, Dr. Builder Muhammad Uba, ya taya Shugaban Karamar Hukumar Dutse, Dr. Sibu Abdullahi murna, bisa samun nasarar zama sabon Shugaban Ƙungiyar Ƙananan Hukumomin Najeriya (ALGON) a Jihar Jigawa.
A wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, Dr. Uba ya bayyana zaben Dr. Sibu a matsayin gagarumar nasara tare da yi masa fatan alkhairi yayin aikinsa.
Ya bayyana kwarin gwiwar cewa jagorancin Dr. Sibu zai ƙarfafa haɗin kai da fahimtar juna tsakanin ƙananan hukumomi 27 na jihar, wanda hakan zai haɓaka samar da ci gaba, tare da inganta tattalin arziki a fadin Jigawa.
Dr. Uba ya kuma yi addu’ar fatan alkhairi ga Jihar Jigawa da shugabanninta domin cimma nasarar manufofin da aka sanya a gaba.
Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu ya yi wa Dr. Sibu fatan samun nasarar shugabanci tare da bayyana tabbacin cewa jagorancinsa zai yi tasiri mai kyau ga al’ummar Jihar Jigawa.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai5 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai6 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai3 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai7 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai5 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
