Connect with us

Labarai

Builder Uba Ya Taya Sabon Shugaban ALGON Na Jihar Jigawa Murna

Published

on

Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu, Dr. Builder Muhammad Uba, ya taya Shugaban Karamar Hukumar Dutse, Dr. Sibu Abdullahi murna, bisa samun nasarar zama sabon Shugaban Ƙungiyar Ƙananan Hukumomin Najeriya (ALGON) a Jihar Jigawa.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, Dr. Uba ya bayyana zaben Dr. Sibu a matsayin gagarumar nasara tare da yi masa fatan alkhairi yayin aikinsa.

Ya bayyana kwarin gwiwar cewa jagorancin Dr. Sibu zai ƙarfafa haɗin kai da fahimtar juna tsakanin ƙananan hukumomi 27 na jihar, wanda hakan zai haɓaka samar da ci gaba,  tare da inganta tattalin arziki a fadin Jigawa.

Dr. Uba ya kuma yi addu’ar fatan alkhairi ga Jihar Jigawa da shugabanninta domin cimma nasarar manufofin da aka sanya a gaba.

Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu ya yi wa Dr. Sibu fatan samun nasarar shugabanci tare da bayyana tabbacin cewa jagorancinsa zai yi tasiri mai kyau ga al’ummar Jihar Jigawa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

 

Labarai

Labarai11 hours ago

Tinubu Ya Nada Ibrahim Masari a Matsayin Mai Ba Shi Shawara Kan Harkokin Siyasa

Daga Bello Wakili Shugaban Ƙasa Bola Tinubu  ya naɗa Ibrahim Aminu Masari a matsayin Mai ba shi Shawara na Musamman...

Labarai11 hours ago

Kungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi

Daga Usman Muhammad Zaria  Wata ƙungiyar al’umma mai suna Hadejia Advocacy ta yaba wa Gwamnan  Jigawa, Umar Namadi, kan yadda...

Labarai17 hours ago

Ramadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu

Daga Yusuf Zubairu Kauru Sarkin Kauru da ke Jihar Kaduna, Alhaji Zakari Ya’u Shehu Usman, ya yi kira da a...

Labarai18 hours ago

Gwamnatin Jigawa Ta Sha Alwashin Bin Kadin Shari’ar Walida Abdulhadi

Daga Usman Muhammad Zaria  Gwamna Umar Namadi ya tabbatar da cewa Gwamnatin  Jigawa za ta bi sawun shari’ar sace ‘yar...

Labarai2 days ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi2 days ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai2 days ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai3 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai4 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Mafi Shahara