Labarai
Ana Gudanar da Zaɓen Shugaban Kasar Senegal
Yan ƙasar Senegal na kaɗa ƙuri’a ranar Lahadi a zaɓen shugaban ƙasar bayan shekaru uku ana tayar da jijiyoyin siyasa sakamakon tuhumar da aka yi wa jagoran ƴan hamayya Ousmane Sonko da kuma fargabar da aka yi cewa shugaban ƙasar zai tsawaita wa’adin mulkinsa.
Ƴan takara 19 ne za su fafata domin neman wanda zai maye gurbin Shugaba Macky Sall, wanda zai sauka daga mulki bayan ya kammala wa’adi biyu.
Mutum miliyan 7.3 ne suka yi rajista a zaɓen sai dai ana ganin fafatawar za ta fi zafi tsakanin ɗan takarar gamayyar jam’iyyu masu mulki firaiminista Amadou Ba da babban ɗan hamayya Bassirou Diomaye Faye.
Dukansu sun taɓa aiki a hukumar karɓar haraji ta ƙasar, sai dai yanzu kowannensu yana da manufofi da suka sha bamban. Ba, mai shekara 62, ya yi alƙawarin ci gaba da tsarin da shugaba mai ci yake kai, yayin da Faye, mai shekara 43 ya sha alwashin kawo gagarumin sauyi.
Kowannensu ya bugi ƙirji cewa zai lashe zaɓen a zagayen farko — sai dai akwai yiwuwar ta tafi zagaye na biyu, domin kuwa akwai ƴan takara 15 a zaɓen, ciki har da mace guda ɗaya.
Za a rufe rumfunan zaɓe ne da misalin ƙarfe shida na yamma a agogon Dakar kuma ana sa ran soma sanar da sakamakon zaɓen da tsakar dare.
Ɗaruruwan masu jami’ai daga Tarayyar Afirka da ECOWAS da kuma Tarayyar Turai ne za su sanya ido kan zaɓen.
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United